Sojojin Kasar Yemen Sun Kai Wa HKI Hari Da Makami Mai Linzami
Published: 19th, March 2025 GMT
A ci gaba da taya Falasdinawa fada da sojojin Yemen suke yi, sun kai wa sansanin jiragen sama na HKI dake saharar “Nakab” hari da makami mai linzami samfurin “Ballistic’ wanda ya fi sauti sauri.
A wata sanarwa da sojojin Yemen su ka yi da marecen jiya Talata sun bayyana cewa; a karkashin taimakawa Falasdinawa da ake zalunta, da kuma mayar da martani akan kisan kiyashin da abokan gaba ‘yan sahayoniya suke yi wa ‘yan’uwanmu a Gaza, sojojin Yemen sun kai hari da yardar Allah akan sansanin sojan sama na Nivatim” da makami mai linzami wanda ya fi sauti sauri, mai suna “Falasdinu 2” sun bisa yardar Allah ya isa inda aka harba shi.
Sanarwar ta kuma ci gaba da cewa; Sojojin Yemen za su fadada hare-haren da suke kai wa a cikin Falasdinu dake karkashin mamaya a cikin sa’o’i da kuma kwanaki masu zuwa, matukar abokan gaba ba su daina kai wa Gaza hare-hare ba.”
Kakakin sojan Yemen janar Yahya Sari ya kuma bayyana cewa; al’ummar Yemen da ta kunshi jagorori, al’umma da kuma soja, ba za su zama ‘yan kallo ba ana yi wa ‘yan’uwanmu kisan kiyashi a Gaza.” Har ila yau janar Sari ya ce; “ Bisa yardar Allah sojojin na Yemen za su yi amfani da dukkanin makaman da take da su domin kare da taimakon Falasdinawa da ake zalunta.”
Janar Sari ya kuma ce; Ba za su daina kai hare-haren ba, har zuwa lokacin da za a dakatar da killace Gaza da ci gaba da kai musu kayan agaji a suke da bukatuwa da su, kuma za su ci gaba da hana jiragen ruwa wucewa zuwa HKI.
A gefe daya, sojojin na Yemen sun sanar da sake kai hari akan jirgin dakon jiragen yaki na Amurka dake cikin tekun “Red Sea” wanda shi ne karo na 4 a cikin sa’o’i 72.
Janar Sari ya kuma sanar da cewa sun yi nasarar dakile wani hari da ake gab da kai wa Yemen ta sama,kuma hare-haren na Amurka ba za su hana su ci gaba da hana su aiki da nauyin da ya rataya a wuyansu ba na addini da ‘yan’adamta dangane da al’ummar Falasdinu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yemen: Amurka Ta Sake Kai Wani Harin A Kasar Yemen
Kasar Yemen ta sanar da cewa Amurka da ta sake kai wasu hare-haren a gundumar Hudaidah akan wani kamfani na auduga.
Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya nakalto majiyar Ansarullah ta kasar Yemen din tana cewa; Sojojin na Yemen sun kai hare-hare da makamai masu linzami har 18 akan jiragen ruwa na dakon jiragen yaki “USS Troman” hari.
Kakakin sojan kasar Yemen ne janar Yahya Sari ya sanar da kai hare-hare na martani akan jiragen yakin Amurka.
Tun daga ranar Asabar din da ta gabata ne dai jiragen yakin Amurka da na Birtaniya su ka rika kai wa Yemen hare-hare da sun yi sanadiyyar shahadar mutane da dama.
Yankunan da harin ya shafa sun hada biranen San’aa da kuma Sa’adah, sai kuma Hudaidai.
A gefe daya shugaban kungiyar Ansarullah ta Yemen Sayyid Abdulmalik Husi, ya ce: hare-haren ta’adanci wadanda sojojin Amurka da Burtaniya suka kai kan yankuna da dama a kasar ba za su hana mutanen kasar ci gaba da kare Falasdinawa a Gaza ba.
Haka nan kuma ya kara da cewa: Za su ci gaba da kai hare hare a kan jiragen HKI da na Burtaniya da na Amurkan, masu wucewa ta tekun malia kamar yadda ta bayyana tun farko.
Kungiyar Ansarullah ta kasar yemen dai ta tallafawa Falasdinawa a yakin tufanul Aksa wanda aka fara a ranar 7 ga watan octoban shekara ta 2023, har zuwa lokacin da aka tsagaita wuta tsakanin Falasdinawa a Gaza da HKI a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025.
Mayakan “Jubhatun-Nusrah’ Na Kasar Syria Sun Kai Hari Akan Iyakar Kasar Leabnon
A jiya Lahadi ne dai kungiyar ta ‘yan ta’adda ta kai hare-hare akan iyakar Lebanon ta yankin Hermul
Ma’aikatar tsaron Syria ta fitar da wata sanarwa da a ciki ta riya cewa; harin nata martani akan wani hari da aka kai a can cikin kasar wanda ta jinginawa HIzbullah, da kuma ya yi sanadiyyar mutumar jami’an tsaro uku.