Shugaban Duruz A Kasar Syria Ya Ki Amincewa Da Sabon Tsarin Mulkin Kasar
Published: 19th, March 2025 GMT
Shugaban na kurdawa a Syira Hikmat al-Hijri ya soki halayyar gwamnatin rikon kwarya ta kasar Syria, tare da nuna kin amincewa da sabon tsarin mulkin kasar da aka sanar kwanaki kadan da su ka gabata.
Hikmata al-Hijri ya yi kira da gyara yadda ake tafiya a yanzu da kuma rubuta sabon tsarin mulki wanda zai zama yana wakiltar dukkanin bangarorin mutanen kasar.
Shugaban na ‘yan Duruz ya bayyana cewa; sabon tsarin mulkin da aka gabatar yana nuni ne da mahangar wani bangare daya na al’ummar kasar, wanda kuma yake share fage na kafa tsarin kama-karya, maimakon kafa tsarin demokradiyya. Haka nan kuma ya ce, ko kadan ba a yi aiki da tsarin da zai kai ga kafa hukuma ba, sannan kuma gwamnatin rikon kwarya ta yi watsi da abinda al’ummar kasar suke son cimmawa ta hanyar juyin da su ka yi.
Dangane da taron kasa da aka yi, shugaban ‘yan Duruz din ya ce, taro ne na sa’o’i 5 kadai wanda kuma ba musayar ra’ayi aka yi ba, an gabatarwa da mahalartarsa umarni ne na abinda ake son yi, don haka gwiwar mutane ta yi sanyi.
Haka nan kuma shugaban na Kurdawa ya zargi kungiyar “Tahrirus-Sham’ da cewa ta damfarawa al’ummar Syria shugabanninta wadanda ba kwararru ba ne, haka nan kuma an kori ma’aikatan gwamnati da dama daga aiki cikin tilasci.
Akan abinda ya faru a gabar ruwan Syria shugaban na ‘yan Duruz ya dorawa gwamnatin alhaki, yana mai yin tuni da cewa, laifukan da aka tafka sun yi kama da wadanda “ Da’esh’ ta aikata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ummar Yemen sun sha alwashin tsayin-daka kan barazanar Trump
Al’ummar kasar Yemen sun gudanar da wani gagarumin ganganmi a fadin kasar, inda suka lashi takobin tinkarar ta’addancin Amurka ta hanyar kara karfin soji, da hada karfi da karfe, da kuma abokan gaba shakat.
Gangamin ya zo ne bayan da jagoran gwagwarmayar kungiyar Ansarullah Abdul Malik al-Houthi ya bayyana cewa kasar a shirye ta ke duk wata barazanar Amurka.
“Ba mu tsoron kowa, kuma ba mu rusuna wa kowa sai Allah. Za mu fuskanci duk wani tashin hankali. ” inji shi
“A shirye muke mu tunkari dukkan azzaluman duniya ba tare da wata fargaba ko tsoro ba.
Abdul Malik al-Houthi ya bayyana hakan ne a wani jawabi da ya yi a ranar Lahadi, kwana guda bayan da Amurka ta kai wasu jerin hare-hare a Sanaa babban birnin kasar Yemen da wasu larduna da dama a fadin kasar, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama da suka hada da mata da kananan yara.
A yammacin ranar Asabar jiragen yakin Amurka da na Birtaniya sun kai hare-hare 47 a wurare da dama a Sanaa babban birnin kasar, da kuma wasu yankunan lardin Saada da ke arewacin kasar, da lardin al-Bayda da ke tsakiyar kasar, da kuma lardin Dhamar da ke kudu maso yammacin kasar, inda akalla mutane 31 sukayi shahada.