Aminiya:
2025-03-19@11:11:18 GMT

HOTUNA: An yi gobara a kasuwar ’yan gwan-gwan da ke Kano

Published: 19th, March 2025 GMT

Wata gobara da ta auku safiyar wannan Larabar ta laƙume kasuwar ’yan gwan-gwan da ke unguwar Dakata a Ƙaramar Hukumar Nassarawa ta Jihar Kano.

Kasuwar wadda ake kira da Kwalema tana nan a kan titin Zango, daura da gidajen man Dominion da kuma Mobil da ke makwabtaka da ofishin Hukumar WAEC.

Cire Gwamna Fubara ya saɓa wa Kundin Tsarin Mulki — Lauyoyi DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna

Mai magana da yawun hukumar kwana-kwana Saminu Yusuf Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa jami’ansu na ci gaba da ƙoƙarin kashe gobarar da ke neman wuce gona da iri.

Sai dai ya bayyana cewa duk da bincike ya soma gudana, amma kawo yanzu ba su gano musabbabin tashin gobarar ba.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Gwangwan Jihar Kano Kwalema

এছাড়াও পড়ুন:

Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana shirin mayar da Filin Idi na Ƙofar Mata zuwa Cibiyar Taro ta Ƙasa da Ƙasa don Harkokin Addinin Musulunci.

Sabuwar cibiyar za ta zama wajen gudanar da taruka da karatuttukan addini maimakon barin filin ana amfani da shi sau biyu a shekara don Sallar Idi.

HOTUNA: NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye a cikin carbi da takalma Akwai ’yan ƙwaya a cikin sarakunan gargajiya — Obasanjo

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wani taron buɗa-baki da ya shirya a Fadar Gwamnatin jihar a ranar 15 ga watan Ramadan.

Taron ya samu halartar Mambobin Majalisar Malamai, inda suka tattauna kan haɗin kai da kuma rawar da malamai ke takawa wajen wanzar da zaman lafiya.

Gwamna Abba ya ce za a kafa harsashin ginin cibiyar makonni biyu bayan Sallar Idi Ƙarama, sannan daga bisani za a miƙa ta ga malamai don su kula da ita.

Baya ga haka, gwamnan ya kuma bayyana aniyarsa na gyara dukkanin masallatan Juma’a a faɗin jihar don tabbatar da cewa sun zama ingantattun wuraren ibada.

Ya umarci Kwamishinan Harkokin Addini da ya tattara sunayen masallatan da ke buƙatar gyara cikin gaggawa.

Hakazalika, gwamnan ya kuma sanar da cewa ana gina sabon babban Masallacin Juma’a a Fadar Gwamnatin jihar domin ƙara wa masu ibada wajen da ya fi girma da dacewa.

Da yake jawabi a madadin sauran malamai, Sheikh Muhammad Nasir Adam, limamin Masallacin Sheikh Ahmad Tijjani, ya yaba da hangen nesan gwamnan.

Taron ya samu halartar mambobin Hukumar Shari’a, Majalisar Zartarwa, da wasu manyan baƙi.

Gwamnan ya tabbatarwa da malaman addini cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da sauraron shawarwarinsu domin tabbatar da zaman lafiya da daidaito a Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarakunan Kano su kimtsa wa hawan sallah bana — Abba
  • DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna
  • Hukumar Alhazan Jihar Jigawa Ta Ware Kujeru 54 Ga Malamai Da Jami’an Kananan Hukumomi
  • Iran ta kuduri aniyar yin hadin gwiwa da hukumar IAEA
  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A Legas  Ya Koma APC Daga PDP
  • EFCC ta kama Murja Kunya kan wulaƙanta takardun Naira
  • Darajar Kasuwar Kayan Aikin Likitancin Kasar Sin Ta Kai Yuan Triliyan 1.35
  • Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci
  • HOTUNA: NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye a cikin carbi da takalma