Harin Jirgin Yakin Sojoji Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 18 A Kasuwa
Published: 19th, March 2025 GMT
Majiyar ‘yan aware ta kasar Mali ta sanar da cewa wani hari da sojojin gwamnati su ka kai a arewacin kasar ya yi sanadiyyar kashe mutane 18 a arewacin kasar Yemen, sai dai sojojin gwamnatin ta ce, ‘yan aware ta kai wa hari.
Kungiyar Azbinawa ‘yan aware ta ce sojojin gwamnatin kasar sun kai hari ne a garin Lerneb mai nisan kilo mita 50 daga birnin Timbuktu, a ranar Litinin da ta gabata kuma bayan mutane 18 da su ka kwanta dama, wasu 7 sun jikkata.
Kungiyar ta Azbinawa ta bayyana abinda ya faru da cewa; “Dabbanci” ne irin na zamanin jahiliyya.
Sai dai sojojin gwamnatin kasar ta Mali sun wallafa a shafinsu na X cewa; sun kai harin ne akan wata tunga ta ‘yan ta’adda tare da kashe 11 daga cikinsu.
Fiye da shekaru 10 kenan kasar ta Mali tare da makwabtanta, Burkina Faso da Nijar suke fada da kungiyoyi masu dauke da makamai da su ka hada al’ka’ida da kuma “Da’esh”.
Bayan juyin mulkin da aka yi a cikin kasashen uku, da korar sojojin Faransa, kasar ta Mali ta gayyato mayakan kungiyar “Wagner” daga kasar Rasha, domin taya ta fada da masu dauke da makaman.
Sai dai a wasu lokutan ana samun kuskure irin wannan da wajen kai wa masu dauke da makamai hari, ake kai wa fararen hula.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato
Rahotanni sun ce an kashe wani uba da ‘ya’yansa biyu a ƙauyen Zogu da ke Gundumar Miango a Ƙaramar hukumar Bassa ta jihar Filato.
Kakakin Ƙungiyar ci gaban Irigwe (IDA), Sam Jugo, wanda ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a Jos, ya bayyana sunayen waɗanda harin ya rutsa da su kamar haka, Weyi Gebeh a mai shekara 56, da Zhu Weyi mai shekara 25 da Henry Weyi mai shekara 16.
‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu An kama mutum 8 kan faɗan daba a KanoA cewar Jugo, an kashe mutanen ne cikin dare a lokacin da suke barci, inda ya bayyana lamarin a matsayin dabbanci.
Ya ce, “An sanar da shugabannin Ƙungiyar ci gaban Irigwe (IDA) game da wani harin da aka kai ƙauyen Zogu, Miango wanda ya yi sanadin mutuwar wani uba da ‘ya’yansa biyu waɗanda suka haɗa da: Weyi Gebeh da Zhu Weyi da Henry Weyi.
“Wannan harin na baya-bayan nan ya kai ga mutuwar mutane tara a cikin makon nan kaɗai, Ƙungiyar IDA ta nuna rashin jin daɗinta game da taɓarɓarewar al’amura a yankin Irigwe tare da yin kira ga jami’an tsaro da su yi duk abin da ya kamata don daƙile wannan ɓarna a yankinmu tare da kama waɗanda suka aikata laifin don fuskantar shari’a.
Kakakin rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Samson Zhakom da rundunar ’yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred, har yanzu ba su mayar da martani ga saƙon da wakilinmu ya aika masu ba.