Ɗan Afirka da yake da ‘ya’ya 104 da jikoki 144
Published: 19th, March 2025 GMT
Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga, wani mutum ne daga wani karamin kauye a Tanzaniya, wanda yake da iyali na musamman.
Ya auri mata 16, yana da ’ya’ya sama da 100 da jikoki 144.
A kwanakin nan, maza da yawa suna ta kokarin samun iyali da neman haihuwa, duk da ana kallon karuwar iyali kamar karin matsin rayuwa ne mai yawa.
Kula da yara sama da biyu ko uku abu ne da ba za a yi tsammani ba ga galibin matasa, amma kuma akwai maza irin su Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga wadanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen fadada iyalansu gwargwadon iko.
Mutumin ɗan asalin wani ƙaramin ƙauye ne da ke Njombe a kasar Tanzaniya, a halin yanzu yana da mata 16, ‘ya’ya 104 da jikoki 144.
Gidansa kamar wani dan karamin kauye ne, inda kowace mace daga cikin matansa take da bangarenta kuma iyalansa suna yawo a ko’ina, suna gudanar da sana’o’i, suna kula da dimbin yara.
A wata hira da ya yi da Afrimax kwanan nan, Ernesto Kapinga ya ce, ya fara fadada iyalinsa ne bisa bukatar mahaifinsa.
Ya auri matarsa ta farko a shekara ta 1961, kuma ya haifi da na farko bayan shekara guda, amma mahaifinsa ya gaya masa cewa, mace daya ba ta isa ba.
Sai ya ce zai ba shi sadaki idan ya amince ya auri karin mata don ya samu haihuwar yara da yawa.
“Danginmu ba su da yawa, ina so ka fadada su,” mahaifin Kapinga ya fada masa, kuma ya amince da hakan.
Mahaifinsa ya biya sadakin matansa biyar na farko, amma bai tsaya nan ba. A ƙarshe Ernesto ya auri mata 20.
Wasu sun zabi barinsa a wani lokaci, wasu kuma sun rasu, amma yau yana zaune da mata 16, bakwai daga cikinsu masu kananan shekaru ne.
Matan Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga sun bayyana cewa, ya kasance miji na gari.
Ɗaya daga cikin matansa ta bayyana wa ’yar’uwarsa irin kyakkyawar rayuwar da take yi tare da shi, don haka suka yanke shawarar zama da shi.
“A nan, kowa yana da rawar da yake takawa,” in ji magidancin.
“Kowace mace tana da gidanta da kicin dinta, babu gasa a tsakaninsu.
“Kowacce ta san wurinta, tare muke noma, muna ci tare, muna aiki tare .
“Wannan ba gida ba ne kawai, tsari ne da ake bi kuma yana aiki.
“To ta yaya mutum zai samar da daruruwan daruwan mutane abincin da za su ci?.
To a fili yake cewa, dukakan iyali suna dogara ne da aikinsu don samun abinci, kuma sun dogara kacokan ga amfanin gonakinsu da dabbobinsu wajen samun abinci.
Suna shuka masara da wake da rogo da ayaba, kuma abin da ya yi rara, sukan yi kasuwancinsa.
“Mutane suna tunanin ina sarrafa komai,” in ji Kapinga.
“Amma gaskiyar magana ita ce, matana suna hada kan wannan iyali, ni kawai ina yi musu jagoranci ne.”
Matan sun bayyana cewa, a koyaushe suna bayyana matsalolinsu kuma ba sa barin fushi ya yi barazana ga hadin kan gida.
Idan ba za su iya daidaita al’amura a tsakaninsu ba, sai su kawo al’amura ga Ernesto kuma ya saurare su, ba ya goyon bayan wani bangare, amma yana ba su shawara kawai.
A bayyane yake, wannan tsarin iyalin yana aiki daidai ya zuwa yanzu.
Wani abin sha’awa shi ne, Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga ya yarda cewa, a wasu lokuta yakan manta sunayen ‘ya’yansa da jikokinsa, yana mai cewa yakan tuna sunayensu 50 daga cikinsu. Ya ce yakan tuna sauran idan ya ga fuskokinsu.
Iyalan Kapinga sun kasance babban dangin da ya fi girma, amma ya rasa yara 40 sakamakon rashin lafiya da hadura.
Yana bakin ciki idan ya tuna da su, amma ya ci gaba da rayuwarsa don yana da ‘ya’ya da yawa a raye wadanda ke bukatar kulawarsa koyaushe.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Mutane Da Yawa Sun Jikkata Bayan Fashewar Bam A Wata Kasuwa A Ikeja
A ranar Juma’a da daddare, wata fashewar bama-bama a wata shahararriyar kasuwa a titin Kodesoh, Ikeja dake Lagos ta janyo raunuka ga mutane da dama. Shaidu sun bayyana cewa fashewar ta faru ne lokacin da wani mai kula da shagon kyamara ya yi kokarin bude wani kunshin da aka kawo.
Hukumar agajin gaggawa, tare da jami’an ‘yansanda daga tashar yankin G, EOD-CBRN Base 23 ta Ikeja, da ma’aikatan hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa na jihar Lagos (LASTMA), sun tura jami’ansu domin gudanar da ayyukan daukar matakai da tsaro a wurin.
Kwalara Ta Kashe Mutane 5 A Lagos, An Kai 60 Asibiti Ranga-Ranga Ƴan Nijeriya 85 Za Su Iso Lagos Daga Amurka A YauWani shaida gani da ido, Lucky Okoro, ya bayyana yadda ya samu damar gudu wa daga wurin fashewar, yana mai cewa, “kawai nayi ƙoƙarin shiga shagon, sai fashewar ta afku. Ban jima ba, sai na ga wutar tana kona wani mutum da wata mata a cikin shagon.” Wani shaidar, Olumide Gbeleyi, wanda yake daga wani otel kusa da wurin, ya bayyana cewa, “Mun ji hayaniyar fashewar kuma muka ga hayaki ya rufe ko’ina. Wata mata tana sayar da kayan ciye-ciye a waje ta ji rauni mai tsanani.”
Sule Aminu, wanda ya bayyana yadda abin da ya sani game da lamarin, ya zargi cewa kunshin mai ban mamaki yana dauke da wani abu da aka tura domin cutar da mai shagon.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp