Aminiya:
2025-03-19@17:05:07 GMT

Ɗan Afirka da yake da ‘ya’ya 104 da jikoki 144

Published: 19th, March 2025 GMT

Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga, wani mutum ne daga wani karamin kauye a Tanzaniya, wanda yake da iyali na musamman.

Ya auri mata 16, yana da ’ya’ya sama da 100 da jikoki 144.

A kwanakin nan, maza da yawa suna ta kokarin samun iyali da neman haihuwa, duk da ana kallon karuwar iyali kamar karin matsin rayuwa ne mai yawa.

DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna An shiga zaman ɗar-ɗar yayin da sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Ribas

Kula da yara sama da biyu ko uku abu ne da ba za a yi tsammani ba ga galibin matasa, amma kuma akwai maza irin su Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga wadanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen fadada iyalansu gwargwadon iko.

Mutumin ɗan asalin wani ƙaramin ƙauye ne da ke Njombe a kasar Tanzaniya, a halin yanzu yana da mata 16, ‘ya’ya 104 da jikoki 144.

Gidansa kamar wani dan karamin kauye ne, inda kowace mace daga cikin matansa take da bangarenta kuma iyalansa suna yawo a ko’ina, suna gudanar da sana’o’i, suna kula da dimbin yara.

A wata hira da ya yi da Afrimax kwanan nan, Ernesto Kapinga ya ce, ya fara fadada iyalinsa ne bisa bukatar mahaifinsa.

Ya auri matarsa ta farko a shekara ta 1961, kuma ya haifi da na farko bayan shekara guda, amma mahaifinsa ya gaya masa cewa, mace daya ba ta isa ba.

Sai ya ce zai ba shi sadaki idan ya amince ya auri karin mata don ya samu haihuwar yara da yawa.

“Danginmu ba su da yawa, ina so ka fadada su,” mahaifin Kapinga ya fada masa, kuma ya amince da hakan.

Mahaifinsa ya biya sadakin matansa biyar na farko, amma bai tsaya nan ba. A ƙarshe Ernesto ya auri mata 20.

Wasu sun zabi barinsa a wani lokaci, wasu kuma sun rasu, amma yau yana zaune da mata 16, bakwai daga cikinsu masu kananan shekaru ne.

Matan Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga sun bayyana cewa, ya kasance miji na gari.

Ɗaya daga cikin matansa ta bayyana wa ’yar’uwarsa irin kyakkyawar rayuwar da take yi tare da shi, don haka suka yanke shawarar zama da shi.

“A nan, kowa yana da rawar da yake takawa,” in ji magidancin.

“Kowace mace tana da gidanta da kicin dinta, babu gasa a tsakaninsu.

“Kowacce ta san wurinta, tare muke noma, muna ci tare, muna aiki tare .

“Wannan ba gida ba ne kawai, tsari ne da ake bi kuma yana aiki.

“To ta yaya mutum zai samar da daruruwan daruwan mutane abincin da za su ci?.

To a fili yake cewa, dukakan iyali suna dogara ne da aikinsu don samun abinci, kuma sun dogara kacokan ga amfanin gonakinsu da dabbobinsu wajen samun abinci.

Suna shuka masara da wake da rogo da ayaba, kuma abin da ya yi rara, sukan yi kasuwancinsa.

“Mutane suna tunanin ina sarrafa komai,” in ji Kapinga.

“Amma gaskiyar magana ita ce, matana suna hada kan wannan iyali, ni kawai ina yi musu jagoranci ne.”

Matan sun bayyana cewa, a koyaushe suna bayyana matsalolinsu kuma ba sa barin fushi ya yi barazana ga hadin kan gida.

Idan ba za su iya daidaita al’amura a tsakaninsu ba, sai su kawo al’amura ga Ernesto kuma ya saurare su, ba ya goyon bayan wani bangare, amma yana ba su shawara kawai.

A bayyane yake, wannan tsarin iyalin yana aiki daidai ya zuwa yanzu.

Wani abin sha’awa shi ne, Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga ya yarda cewa, a wasu lokuta yakan manta sunayen ‘ya’yansa da jikokinsa, yana mai cewa yakan tuna sunayensu 50 daga cikinsu. Ya ce yakan tuna sauran idan ya ga fuskokinsu.

Iyalan Kapinga sun kasance babban dangin da ya fi girma, amma ya rasa yara 40 sakamakon rashin lafiya da hadura.

Yana bakin ciki idan ya tuna da su, amma ya ci gaba da rayuwarsa don yana da ‘ya’ya da yawa a raye wadanda ke bukatar kulawarsa koyaushe.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Abba ya rantsar da sabon Kwamishinan Gidaje na Kano

Gwamna Abba Kabir Yusuf a wannan Litinin ɗin ya rantsar da sabon Kwamishinan Ma’aikatar Tsarawa da Bunƙasa Gidaje ta Kano, Ibrahim Yakubu Adamu.

Wannan dai shi ne karo na huɗu cikin ƙasa da shekaru biyu ke nan da gwamnan yake faɗaɗa majalisar zartarwa jihar ta Kano.

Ana zargin wa da ƙani da yi wa almajiri yankan rago a Adamawa Majalisar Ribas ta soma shirye-shiryen tsige Gwamna Fubara

Aminiya ta ruwaito cewa gabanin wannan sabon naɗin, Ibrahim Yakubu Adamu shi ne Shugaban Hukumar Tsara Birane ta Kano KNUPDA.

Antoni Janar kuma Kwamishinan Shari’a na Kano, Haruna Isah Dederi ne ya jagoranci rantsar da sabon Kwamishinan da aka gudanar a fadar Gwamnatin Kano.

Da yake jawabi, Gwamnan ya yaba wa sabon kwamishinan wanda ya ba da shaida kan ƙwazo da kuma ƙwarewa haɗi da gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban birnin na Dabo.

Gwamnan ya buga misali da yadda sabon kwamishinan ya jagoranci aikin tsarawa da kuma bunƙasa rukunin gidajen nan na Kwankwasiyya da Amana da Bandirawo waɗanda aka gina a tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015 a zamanin gwamnatin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Sabon kwamshinan wanda ƙwararren mai zana gine-gine ne, Gwamnan ya hikaito yadda ya taka rawar gani wajen tsarawa da kuma aiwatar da wasu muhimman ayyukan gine-gine a lokacin da yake Kwamishinan Ayyuka da Gidaje a tsakanin shekarar 2011 zuwa 2015.

A wani labarin mai nasaba da wannan, Gwamnan ya umarci duk waɗanda suka mallaki gida a rukunin gidaje na Kwankwasiyya ko Amana ko Bandirawo da su tabbatar sun tare nan da watanni uku ko kuma su sanya ’yan haya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba tarbiyya nake koyarwa ba — Sadiq Sani Sadiq
  • HKI Ta Tilastawa Iyalai 10 Ficewa Daga Gidajensu A Sansanin ‘Yan Hijira Na Nabilus
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]
  • Trump Zai Tattauna Da Putin Kan Kawo Ƙarshen Yaƙin Ukraine
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [10]
  • Abba ya rantsar da sabon Kwamishinan Gidaje na Kano
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [9]
  • IRGC: Iran ba za ta fara yaki ba amma za ta mayar da martani ga duk wata barazana
  • Afirka Ta Kudu Ta Caccaki Amurka Kan Korar Jakadanta Daga Washington