Leadership News Hausa:
2025-03-19@17:17:27 GMT

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Published: 19th, March 2025 GMT

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Wani mazaunin yankin ya koka da yadda ‘yan bindiga ke yawan kai hare-hare a waɗannan wurare, lamarin da ya sa jama’a ke cikin fargaba.

A Farin-Shinge, mazauna yankin sun nuna koka kan hare-haren da ke ci gaba da faruwa, inda suka roƙi gwamnati da hukumomin tsaro su ɗauki matakin gaggawa.

Kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da harin kuma ya ce za su binciki lamarin.

Sai dai, har zuwa lokacin da aka haɗa wannan rahoto, ba a samu ƙarin bayani daga ‘yansanda ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina

Dakarun Sojin Najeriya sun kashe ’yan bindiga 31 tare da lalata sansaninsu a Jihar Katsina, yayin wasu hare-hare guda biyu da suka kai.

A farmaki na farko, dakarun Operation Fansan Yamma sun yi artabu da ’yan bindiga a garin Maigora da ke Ƙaramar Hukumar Faskari.

Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka

Da farko, sojojin sun kashe ’yan bindiga biyar bayan sun kai farmaki garin.

Sai dai lokacin da suka sake haɗuwa don kai harin ramuwar gayya, sojojin sun sake kashe guda bakwai, ciki har da Dogo, wanda babban Kwamanda ne a cikinsu.

Haka kuma, sojojin sun ƙwace babura guda bakwai da ‘yan bindigar ke amfani da su.

A wani farmakin, rundunar sojojin sama ta yi luguden wuta a maboyar ’yan bindiga da ke dajin Unguwar Goga, Ruwan Godiya, a Ƙaramar Hukumar Faskari.

Sun lalata sansanin shugabannin ’yan bindiga biyu; Alhaji Gero da Alhaji Riga, inda suka kashe aƙalla mahara 19.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa sojojin Najeriya na ƙara ƙaimi wajen murƙushe ’yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma, tare da lalata sansaninsu.

Har ila yau, sojojin na ci gaba da sintiri ta sama da ƙasa don daƙile yunƙurin ’yan bindiga na sake hare-hare.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ribas: Fubara Ya Fice Daga Gidan Gwamnati Yayin Da Sabon Shugaba Ke Shirin Karɓar Mulki
  • ’Yan Banga Sun Ceto Mutum 3 Daga Hannun ’Yan Bindiga A Taraba
  • Atiku Ya Soki Tinubu Kan Ayyana Dokar Ta-ɓaci a Jihar Ribas
  • Shugaba Tinubu Ya Dakatar Da Gwamnan Jihar Rivers Da ‘Yan Majalisar Dokokin Jihar
  • Mutum 330 Sun Mutu Yayin da Isra’ila Ta Kai Wa Gaza Sabbin Hare-hare 
  • Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
  • Gwamnatin Kano Ta Umarci Ma’aikatanta Da Su Tantance Allbashin Watan Maris Kafin A Biya Su
  • Me Ya Sa Ba Za a Ba Yankin Taiwan Damar Samun ‘Yancin Kai Ba?
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina