Aminiya:
2025-04-13@10:57:56 GMT

Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin Ribas 

Published: 19th, March 2025 GMT

Gwamnan Jihar Ribas da aka dakatar, Similanayi Fubara, ya fice Fadar Gwamnatin Jihar da ke Fatakwal.

Majiyoyi sun shaida wa Aminiya cewa Fubara ya fice daga Fadar Gwamnatin da safiyar Laraba, a daidai lokacin da sabon Shugaban Riƙn Ƙwarya, Admiral Ekwe Ibas (mai ritaya), ke shirin karɓar ragamar mulki.

Ɗan Afirka da yake da ‘ya’ya 104 da jikoki 144 Sarakunan Kano su kimtsa wa hawan sallah bana — Abba

Wakilin Aminiya ya ziyarci Fadar Gwamnatin, inda ya lura cewa akwai kwanciyar hankali a yankin, inda aka girke motocin yaƙi guda uku a kofar shiga gidan gwamnatin.

Wani jami’in tsaro ya tabbatar da cewa an sauya dukkanin jami’an tsaron da ke aiki a Fadar Gwamnatin Jihar.

“Gwamna ya fice daga ciki, kuma muna jiran sabon shugaba ya iso. Komai na tafiya lafiya,” in ji shi.

A halin yanzu, al’ummar Fatakwal na ci gaba da harkokinsu yadda suka saba ba tare da wata matsala ba.

Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas a ranar Talata, sakamakon ikicin siyasa da ya dabaibaye jihar.

Sai dai matakin na Shugaban Ƙasa, ya bar baya da ƙura inda mutane ke tofa albarkacin bakinsu kan lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara rikicin siyasa Fadar Gwamnatin

এছাড়াও পড়ুন:

USAID Za Ta Dawo Aiki A Wasu Ƙasashen Duniya – Gwamnatin Amurka

A cewar mai magana da yawun Ma’aikatar Cikin Gida ta Amurka, Tammy Bruce, akwai damuwa kan taimakon da ke iya faɗa wa hannun ƙungiyoyin Taliban da Houthi, waɗanda ke iko da mafi yawan yankunan waɗannan ƙasashe.

A baya-bayan nan, Hukumar Yaƙi da Yunwa ta Duniya (WFP) ta bayyana cewa katse tallafin Amurka tamkar “hukuncin kisa ne” ga miliyoyin mutane da ke fuskantar matsananciyar yunwa a faɗin duniya, musamman a yankunan da ake rikici.

Masu fashin baƙi na ganin wannan mataki na iya taimaka wa dubban mutane, amma kuma har yanzu ana buƙatar a duba inda taimakon ke zuwa don tabbatar da cewa yana taimaka wa mabuƙata ba tare da faɗa wa hannun ‘yan tada ƙayar baya ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hizbullah ta kirayi gwamnatin Lebanon da ta dauki mataki kan hare-haren Isra’ila
  • Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar
  • An Kafa Dokar Kai Da Komowa A Kudancin Kasar Syria
  • Za a mayar da tubabbun ’Yan Boko Haram cikin al’umma – Gwamna Buni
  • Gwamnatin Sakkwato na biyan mafi ƙarancin albashin N70,000 – NLC
  • Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta
  • Sudan ta kai karar Hadaddiyar Daular Larabawa a Kotun ICJ
  • Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki a NUPRC — Buba Galadima
  • Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki NUPRC — Buba Galadima
  • USAID Za Ta Dawo Aiki A Wasu Ƙasashen Duniya – Gwamnatin Amurka