Leadership News Hausa:
2025-03-19@21:35:21 GMT

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Sayar Da Man Fetur A Naira

Published: 19th, March 2025 GMT

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Sayar Da Man Fetur A Naira

Matatar man Dangote ta sanar da dakatar da sayar da man fetur a naira. Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da matatar ta aika wa abokan huldarta a yammacin ranar Laraba. ‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja El-Rufai Ya Shiga Tsilla-tsilla Bayan Rasa Kujerar Minista – APC A cikin sanarwar, Matatar ta ce, wannan matakin na wucin gadi ne, inda ta bayyana dalilin da ya sa aka dauki matakin domin samar da daidaito tsakanin farashin danyen mai da aka siyo da Dala da kuma na Naira.

“Muna so mu sanar da ku cewa, matatar man Dangote ta dakatar da sayar da man fetur a Naira na wani dan lokaci domin kauce wa rashin daidaito tsakanin danyen man da ke wurinmu wanda a halin yanzu ke kan farashin dalar Amurka. “Ya zuwa yanzu, cinikin man fetur da muke samu a Naira ya zarce na danyen man da muka samu a farashin Naira, a sakamakon haka, dole ne mu daidaita kasuwancinmu na dan lokaci. “Muna ci gaba da jajircewa wajen ci gaba da bai wa ‘yan kasuwannin Nijeriya kayayyakinmu mai inganci da zarar mun samu danyen man fetur daga kamfanin NNPC, nan take za mu dawo da cinikin man fetur a Naira”.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: man fetur a Naira

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Ya Dakatar Da Gwamnan Jihar Rivers Da ‘Yan Majalisar Dokokin Jihar

Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-baci a Jihar Rivers, inda ya dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara, da mataimakiyarsa Ngozi Odu, da dukkan mambobin Majalisar Dokokin Jihar na tsawon watanni shida.

A wani jawabi da ya yi  ga alummar kasa ta kafafen yada labarai a ranar Talata, Shugaban kasan ya bayyana cewa an dauki wannan matakin ne sakamakon rikicin siyasa wanda ya ki ci ya ki cinyewa  a jihar, ya kuma hana gudanar da gwamnati yadda ya kamata kuma ya tauye wa jama’ar Jihar Rivers morar romon  dimokuradiyya.

Shugaban kasan ya nuna damuwarsa kan “mummunan hali” da jihar ke ciki, wanda ya kara muni bayan rushewar ginin Majalisar Dokokin Jihar da gwamnan ya yi a ranar 13 ga watan Disambar 2023. A cewarsa, duk da kokarin da ‘yan Najeriya masu kishin kasa suka yi don samun sulhu, rikicin ya ci gaba da tsananta.

Da yake magana kan hukuncin Kotun Koli na ranar 28 ga Fabrairu, 2025, wanda ya zargi gwamnan da aikata ayyukan da suka saɓa wa kundin tsarin mulki da raina doka, Shugaban kasa ya ce, “Babu gwamnati a Jihar Rivers, domin bangaren zartarwa ya rushe majalisar dokoki kuma yana mulki tamkar  mulkin danniya.”

Shugaban kasan ya kuma bayyana cewa ya samu rahotannin tsaro da ke nuna barazana ga kadarorin kasa, ciki har da lalata bututun mai da wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu biyayya  ga gwamnan ne suka aikata, ba tare da daukar wani mataki  don dakile su ba.

Shugaban kasan ya nada tsohon Hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Ibokette Ibas (Rtd), a matsayin mai kula da harkokin Jihar Rivers. Ya bayyana cewa bangaren shari’a na jihar zai ci gaba da aiki kamar yadda ya saba, sannan sabon mai kula da jihar zai kasance yana tsara dokoki ne kawai da amincewar Majalisar Zartarwa ta Tarayya.

Shugaban kasan ya nuna fatan cewa wannan mataki zai tilasta dukkan bangarorin da abin ya shafa a Jihar Rivers su bi dokokin mulki tare da dawo da zaman lafiya.

Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • EFCC Ta Cafke Akanta-janar Na Jihar Bauchi Kan Zargin Badaƙalar Naira Biliyan 70
  • Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira
  • DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna
  • Sashen Masana’antun Dijital Na Kasar Sin Ya Samu Karin Riba Da Ci Gaba A Shekarar 2024
  • Shugaba Tinubu Ya Dakatar Da Gwamnan Jihar Rivers Da ‘Yan Majalisar Dokokin Jihar
  • EFCC Ta Ƙwato Naira Biliyan 365.4 A Shekarar 2024
  • Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Nacewa Ga Samun Ci Gaba Mai Inganci Yayin Ziyararsa A Guizhou
  • Gwamna Yusuf Ya Yi Barazanar Ƙwace Lasisin Jerin Gidajen Kwankwasiyya, Amana Da Bandirawo 
  • Sojojin Sudan sun sanar da samun gagarumin ci gaba a tsakiyar Khartoum