Sabon Kawancen Jihohin Arewacin Najeriya Da Kamfanonin Sin Zai Fa’idantar
Published: 20th, March 2025 GMT
A dunkule, ayyukan da wadannan kamfanoni za su gudanar sun kunshi samar da wadataccen takin zamani da fasahar noma ta zamani, da dabarun sarrafa takin gargajiya da fasahar kiwo mafi dacewa da jihar. Haka nan, kawancen nasu zai hada har da amfani da fasahohin zamani wajen kyautata sha’anin tsaro, da harkokin sufuri da bangaren hidindimun jama’a, da sauran dabaru da tsare-tsare na kwarewar aiki da za a samar a jihar.
Hakika wannan kawance zai fa’idantar sosai saboda yadda yankin na arewa ya kwashi tsawon wasu shekaru yana kaka-ni-ka-yi da matsalolin dake tarnake ci gabansa sakamakon mummunar matsalar tsaro musamman ma a jihar Zamfara wadda ta zama babbar tungar ’yan bindiga.
Kwararru a fannin sha’anin tsaro, sun sha nanata cewa matukar ana so a magance matsalar tsaron da ta hana arewacin Najeriya sakat dole sai an hada da magance zaman kashe wando, da bunkasa tattalin arziki da kuma samar da na-gartaccen ilimi.
Sabon yunkurin jihohin arewa na kulla kawance da kamfanonin Sin babu shakka zai bude kofofin karfafa tattalin arzikin yankin wanda Allah ya albarkace shi da kasar noma mai kyau fiye da sauran sassan Najeriya, sannan ga tarin albarkar yawan jama’a, da albarkatun sarrafa sabbin makamashi, domin kamfanonin Sin suna da kwarewar aiki da dimbin ayyuka na fasahar zamani ta yadda suke iya sarrafa albarkatu kalilan a samar da amfani mai yawa. Sannan suna da karfin zuba jari fiye da yadda ake zato, domin ko a watan Satumban 2024, gwamnatin jihar Neja da ke arewacin Najeriya ta rattaba hannu da wasu kamfanonin Sin guda biyu –COVEC da CREC a kan kwangilar dala miliyan 684 domin gudanar da ayyukan gona na musamman a jihar.
Tabbas, jihohin sun dauki hanya mai kyau da za ta fa’idantar, fatana shi ne a wayi gari yankin arewa ya dawo da martabarsa ta ci gaban tattalin arziki da kyautata rayuwar al’umma.(Abdulrazaq Yahuza)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Me Ya Sa Ba Za a Ba Yankin Taiwan Damar Samun ‘Yancin Kai Ba?
Sai dai hukumar yankin Taiwan na ci gaba da kokarin yada karairayi, tare da tunasar da kowa kasancewarta. In ba haka ba, wadannan bayanai masu kunshe da kurakurai da muka ambata ba za su bayyana a kan wata jaridar Najeriya ba. Hakika, a shekarun nan, hukumar Taiwan ta yi ta kokarin takala da batun neman “‘yancin kan Taiwan”, lamarin da ya haifar da mummunar barazana ga zaman lafiyar shiyyar da yankin ke ciki. Kamar ba su cika lura da dokar kin barakar kasa ta kasar Sin, wadda aka fara aiwatar da ita wasu shekaru 20 da suka wuce ba. Sai dai an tanada a cikin dokar da cewa, babban yankin kasar Sin zai nuna cikakken sahihanci, da iyakacin kokarin tabbatar da dinkuwar kasa ta hanyar lumana, amma zai dauki kwararran matakan da suka wajaba, idan masu neman “‘yancin kan Taiwan” sun wuce gona da iri.
Tabbas za a tabbatar da dinkuwar kasar Sin waje guda. Yadda masu neman balle yankin Taiwan ke ta da zaune-tsaye ba zai haifar musu da da mai ido ba, illa sanya su gamuwa da ajalinsu cikin sauri. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp