Kungiyar Hamas Ta Ce Falasdinawa Ba Za Su Bar Kasarsu Ba, Ko Da Son Ransu Ko Da Karfi
Published: 20th, March 2025 GMT
Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza ta bada sanarwan cewa mutanen Gaza ba za su taba barin kasarsu ba, da son ransu ko da karfi zuwa wani wuri ba, sai zuwa birnin Qudus babban birnin kasar Falasdinu.
Tashar talabijin ta Presstv ya nakalto kungiyar na fadar haka a jiya Laraba. Ta kuma kara da cewa duk abinda HKI da babbar kawarta Amurka zasu yi don fiddasu daga kasarsu ba zai kai ga nasara ba da yardar All…
Tun shekara 1948 ne kasar Burania a lokacin, wacce ta mamaye kasar Falasdinu ta mikawa yahudawan Sahyoniyya kasar Falasdinu, sannan suka kara mamayar kasar bayan yakin shekara 1967.
Tun lokacin ne Falasdinawa suke gwagwarmaya don kawo karshen mamayar.
A yakin baya-bayan nan dai, wanda aka fara a cikin watan Octoban shekara ta 2023, yahudawan sun kashe falasdinawa kimani 48,000 a gaza kadai, don korar Falasdinawa daga yankin, amma bayan sun kasa korarsu sai aka tsagaita wuta tsakaninsu a cikin watan Jenerun wannan shekarar. Amma a makon da ya gabata yahudawan suka yi watsi da yarjeniyar suka koma yaki da nufin korarsu daga Gaza , a wannan karon tare da taimakon kai Amurka kai tsaye.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran : Zamu fifita diflomasiyya da kasashe makwabtanmu
Iran ta ce za ta fifita diflomatisyya ta tsakaninta da kasashe makobtanta na yankin.
Ministan harkokin wajen kasar ne Abbas Araghchi ya jaddada aniyar kasar kan harkokin diflomasiyya a yankin, yana mai bayyana cewa kasashen da ke makwabtaka da kasar na cikin tsarin Jamhuriyar Musulunci.
“Makwabtanmu sune fifikonmu,” in ji ministan harkokin wajen Iran a cikin wani sako da aka wallafa a shafinsa na X.
Mista Araghchi ya tattauna da takwarsana na Omani, Badr bin Hamad Al Busaidi, a Muscat, babban birnin kasar Omani, inda suka tattauna muhimman batutuwan da suka shafi kasashen biyu da na shiyya-shiyya.
Babban burinmu shi ne kare zaman lafiya da kwanciyar hankali ta hanyar diflomasiyya.
Ziyarar ta Araghchi a birnin Muscat na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin yankin ke ci gaba da ruruwa, sakamakon kisan kiyashin da gwamnatin Isra’ila tare da goyon bayan Amurka ke aiwatarwa a zirin Gaza da kuma yadda ake ci gaba da kai munanan hare-hare a wasu wurare a yankin musamman a Syria da Lebanon.