A ranar 19 ga watan Maris na ko wace shekara ne mutanen Iran suke gudanar da bukukuwan tunawa da ranar da mutanen kasar tare da taimakon gwamnatin lokacin suka sami nasarar kwace kamfanin haka da sarrafa man fetur na kasar, daga hannun wani kamfanin mai na kasar Burtaniya suka maida shin a kasa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya ce , wannan rana abin alfakhari ne ga mutanen kasar, don bayan haka ne kasar ta sami ikon kawo ci gaban tattalin arzikin kasar da kuma shimfida harsashen samun yencin kasar daga hannun kasashen yamma wadanda suka mamaye bangarori da dama a cikin al-amuran kasar.

A ranar 19 ga watan Maris na shekara ta 1951 ne, wato shekaru 78 da suka gabata,  firai ministan kasar Iran na lokacin Dr Muhammad Musaddiq tare da taimakon malaman addini ya sami nasarar kwace kamfanin man fetur na kasar daga hannun turawan ingila ya maida shi na kasa.

Majalisar dokokin kasar Iran ta amince da dokar maida kamfanin ya zama ta kasa a ranar 17 ga watan Maris na shekara ta 1951, sannan majalisar dattawan kasar ta amince da Ita a ranar 19 ga watan Maris na shekarar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ga watan Maris na

এছাড়াও পড়ুন:

Tattalin Arzikin Al’Ummar Kasar Sin Na Tafiya Yadda Ya Kamata A Watan Jarairu Da Fabrairu

Yau Litinin da safe, ofishin yada labarai na majalisar gudanarwa ta Sin ya kira wani taron manema labarai, inda kakakin hukumar kididdiga ta Sin, Fu Linghui ya yi bayani kan yadda tattalin arzikin kasar ke gudana a cikin farkon watanni biyu na bana da suka gabata.

Kididdiga na nuna cewa, daga watan Janairu zuwa Fabrairu na bana, masana’antar samar da kayayyaki na samun saurin bunkasa, inda ribar da kamfanoni da masana’antu da ke iya samun ribar da ta zarce dala miliyan 2.7 a duk shekara, ta karu da kashi 5.9% bisa na makamancin lokacin bara.

Daga cikinsu, masana’antar ba da hidima ta fi samun bunkasuwa, inda alkaluman ci gabanta suka karu da kashi 5.6% bisa na makamancin lokacin bara, kuma adadinsu shi ma ya karu da kashi 0.4% bisa na bara. Dadin dadawa, saurin sayar da kayayyaki a kasuwa ya karu matuka, ta yadda bangaren samar da kayayyaki da zuba jari ga sana’o’in kirkire-kirkire da sabbin fasahohi suka fi samun saurin bunkasuwa. Kazalika, shige da ficen kayayyaki na samun bunkasa ba tare da tangarda ba, kuma yanayin samar da guraben ayyukan yi na samun habaka yadda ya kamata, yayin da kuma farashin kayayyaki ke raguwa idan aka kwatanta da na makamancin lokacin bara.

A takaice dai, a wadannan watanni biyu da suka gabata, tattalin arzikin al’ummar Sinawa na bunkasa yadda ya kamata da samun ci gaba a kai a kai, duba da cewa ana ta aiwatar da kyawawan manufofi daga manyan fannoni. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane Fiye Da 30 Ne Suka Rasa Rayukansu A Lokacinda Motar Dawkar Gas Ta Yi Bindiga A Abuja Na Tarayyar Najeriya
  • MDD Ta Zargi Kasar Rasha Da Aikata Laifukan Yaki A Ukraine
  • Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira
  • DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna
  • An Ware Sama Da Naira Biliyan 1.5 Don Fara Aiki A Sabon Kamfanin Injinan Noma Na Jigawa
  • Tsofaffin furodusoshin Kannywood da aka daina jin ɗuriyarsu
  • Tattalin Arzikin Al’Ummar Kasar Sin Na Tafiya Yadda Ya Kamata A Watan Jarairu Da Fabrairu
  • Iran : Zamu fifita diflomasiyya da kasashe makwabtanmu
  • Al’ummar Yemen sun sha alwashin tsayin-daka kan barazanar Trump