Jakadan Amurka Ya Ziyarci Sarkin Zazzau Domin Karfafa Alakar Amurka Da Najeriya
Published: 20th, March 2025 GMT
Jakadan Amurka a Najeriya, Richard Mills Jr, ya ziyarci mai martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmad Bamalli domin ingantawa da karfafa hadin kan al’adu.
Jekadan ya ce Amurka ta jajirce sosai kan alakar da Najeriya ya kara da cewa; ‘ muna so mu zurfafa shi kuma mu ƙarfafa shi.”
A cewarsa, hanyar da ta fi dacewa wajen zurfafa wannan alaka ita ce ta haduwa irin wannan da za mu ji ta bakin juna.
“Ina sa ran jin ta bakinku kan abubuwan da kuke yi na karfafa hadin kan addini a tsakanin al’umma, damar ilimi da kuma damar yin aiki ga jama’ar ku.
“Abin da Amurka za ta iya yi don haɓaka ƙarin alaƙa da kuma matakan da za mu iya ɗauka don zurfafa dangantakarmu,” in ji Mills.
Da yake mayar da jawabi, Mai martaba Sarkin Zazzau ya yabawa ma’aikatar harkokin wajen Amurka kan bude cibiyar kula da harkokin a Amurka a jami’ar Ahmadu Bello.
Bamalli ya yi fatan wannan cibiar da aka kira da Window on America da turanci ta zama matakin samar da ingantacciyar dama tsakanin Amurka da masarautar Zazzau da jihar Kaduna.
Ya kara da cewa masarautar na da alaka mai tsawo da ofishin jakadancin Amurka inda ya kara da cewa tawagogin ofishin jakadanci sun kasance suna halartar Dabar karshen watan Ramadan a Zariya.
“Amma hakan ya tsaya cik tsawon wasu shekaru saboda rashin tsaro, amma za mu iya cewa zaman lafiya ya dawo ga al’ummarmu.
“Saboda haka, muna fatan mambobin ofishin jakadancin da sauran jami’an diflomasiyya za su ci gaba da halartar bukukuwan Sallah Durbar,” in ji Bamalli.
COV/ Ibrahim Suleiman
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Dattawan Arewa ya ajiye sarautar Magajin Rafin Zazzau
Shugaban Majalisar Dattawan Arewa (NEF), Farfesa Dahiru Ango Abdullahi Yakawada, ya yi murabus daga sarautar Magajin Rafin Zazzau.
Farfesa Dahiru Ango Abdullahi ya yi murabus ne daga sarautar Magajin Rafin Zazzau saboda shekarunsa da suka ja.
Hamas ta ɗora alhakin harin da Isra’ila ta kai a kan Amurka Majalisar Wakilai ta amince da ƙudirin dokar harajiWakilinmu ya ruwaito cewa a yanzu ƙaninsa, Alhaji Shehu Abdullahi Yakawada ne zai gaje shi a wannan kujera
ta hakimanci.
Farfesa Ango Abdullahi yana ɗaya daga cikin mazan jiya da suka yi ragowa a Nijeriya.
Farfesa Dahiru Ango Abdullahi ɗaya ne daga cikin dattawan da al’umma suke buƙata musamman a wannan zamani.
Yana ɗaya daga cikin masu bayyana ra’ayin su a kowanne irin yanayi don jawo hankalin shugabanni da al’ummomi da nufin kyautata rayuwa.
Kazalika, Farfesa Ango Abdullahi shi ne na biyar a tarihin cikin jerin waɗanda suka riƙe muƙamin shugaban jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya.
Tuni dai Masarautar Zazzau ta bayyana Alhaji Shehu Abdullahi Yakawada wadda ƙani ne ga shi Farfesa Dahiru Ango Abdullahi a matsayin sabon Magajin Rafin Zazzau.
Sai dai masarautar ta ce zuwa nan gaba kaɗan za ta fidda ranar da za a yi bikin naɗin sabon Magajin Rafin Zazzau.