Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-13@09:18:53 GMT

Gobara Ta Babbake Wani Shago A Jihar Kwara

Published: 20th, March 2025 GMT

Gobara Ta Babbake Wani Shago A Jihar Kwara

Wata gobara da ta tashi da sanyin safiya ta kone wani shago a wani gini mai daki 13 da ke rukunin gidajen Ile-Lodo a cikin garin Etan a karamar hukumar Ekiti a jihar Kwara.

 

A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar kashe gobara ta jihar Kwara, Hassan Adekunle ya fitar, ya ce bayan an samu tashin gobarar ta kira motar kashe gobara da ma’aikatanta sun isa wurin da gaggawa domin shawo kan gobarar, wadda ta kone wani shago a gaban wani gini mai daki 13.

 

A cewarsa duk da tsananin gobarar, jami’an kashe gobara sun yi taka-tsan-tsan, inda suka dakile tare da kashe wutar kafin ta bazu zuwa wasu gine-ginen da ke kusa.

 

Sanarwar ta bayyana cewa binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa wutar lantarki ce ta haddasa gobarar.

 

Daraktan hukumar kashe gobara ta jihar Kwara, Prince Falade John, ya jajanta wa mai shagon da abin ya shafa, ya kuma yi addu’ar Allah ya mayar musu da asarar da suka yi.

 

Ya kuma jaddada mahimmancin bin matakan tsaro don kaucewa faruwar al’amura a nan gaba.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gobara Kwara kashe gobara

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja

Ana fargabar matafiya da dama sun rasu bayan kifewar wani  kwalekwale ɗauke da ’yan kasuwa a yankin Kogin Neja.

Hatsarin kwalekwalen ya auku ne ƙauyen Sokun da ke yankin Ƙaramar Hukumar Lapai, a sakamakon iska mai ƙarfi da ta haddasa juyawar igiyar ruwan.

Shaidu sun ce hatsarin ya auku ne a yayin da kwalekwalen ke ɗauke da fasinjoji da kuma buhunan shinkafa kimanin 200 daga ƙauyen Bugge na Jihar Kogi a zuwa ƙauyen Sokun na Jihar Neja a ranar Laraba da dare.

Wani mazaunin yankin, Baba Alhassan, ya shaida wa wakilinmu cewa, ba a kai ga tantance ainihin yawan fasinjojin da ke cikin kwalwkwalen a lokacin da lamarin ya faru ba, amma an yi asarar duk buhunan shinkafar a hastarin.

NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya

Ya bayyana cewa daga cikin mamatan har da wani mai sana’ar POS da ƙaninsa ’yan asalin ƙauyen Alaba da ke Ƙaramar Hukumar Lapai

Daraktan Hukumar ba da Agajin Gaggawa na Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa ana ci gaba da aikin ceto da ƙoƙarin gano ainihin musabbabin hatsarin da kuma irin asarar da ta haifar.

Mazauna yankin sun bayyana cewa, “Sufurin ruwa shi ne kaɗai hanyar da ta rage da muke amfani da ita domin kai kayanmu kasuwanni saboda hanyar ta yi mummunan lalacewa.”

Wata ’yar kasuwa a yankin mai suna Fatima Muhammad, ta bayyana cewa, saboda nisan tafiyar, fasinjoji sukan yi tafiyar dare domin su isa kasuwa washegari da safe.

Fatima ta ce, “Babban ƙalubalen da muke fuskanta shi ne sufuri. Da kwalekwale muka dogara wajen kai kayanmu kasuwa. Wani lokaci kwalekwalen na ɗaukar lodi fiye da kima. Sai ka ga kwalekwale mai ƙarfin ɗaukar mutane 100 ya kwashi sama da haka. Amma ban ga laifin fasinjojin ba, musamman masu son su isa da wuri.”

Jama’ar yankin sun yi kira ga Gwamnatin Jihar Neja da ta Tarayya da su samar da wadatattun rigunan kariya da jiragen ruwa na zamani sannan su aiwatar da tsauraran hukunci kan masu karya doka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  • Sanƙarau: An tabbatar da ɓullar cutar ga mutane 300 a Sokoto
  • Gobara Ta Ƙone Shaguna 12 A Kasuwar Siminti Ta Oyo
  • Sabon Kwamishinan Na Kwara Ya Sha Alwashin Dakile Laifuka
  • ’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja
  • Hisbah ta warware rigingimu 565 da lalata katan 51 na barasa a Yobe
  • UBEC Ta Yaba Wa Jigawa Kan Inganta Harkar Ilimi A Jihar
  • Malaman Makarantun Firamare 1,800 Sun Samu Horo Aka A Kwara
  • An Sace Dalibin Jami’ar Tarayya Birnin Kebbi