Sabon kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Ibrahim Bakori, ya sha alwashin yin aiki da gaskiya domin inganta tsaron rayuka da dukiyoyi.

 

CP Bakori ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar hukumar dake Bompai Kano.

 

CP Bakori, wanda kwanan nan ya karbi mukamin kwamishinan ‘yan sanda na 47 a jihar, ya ce daga cikin abubuwan da ya sa a gaba sun hada da magance ‘yan daba da kuma laifuka.

 

CP Bakori ya bayyana matsalar ‘yan daba, fadan daban, satar wayar hannu, da shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasa.

 

Sabon Kwamishinan ya jaddada muhimmancin aikin ‘yan sandan al’umma, da nufin karfafa alaka tsakanin jami’an tsaro da jama’a.

 

Nadin na CP Bakori ya biyo bayan karin girma da aka yi wa magabacinsa zuwa mukamin mataimakin sufeto-Janar na ‘yan sanda (AIG). Da dimbin gogewarsa da jajircewarsa wajen inganta tsaro, mazauna Kano za su iya sa ran samun yanayi mai aminci da tsaro a karkashin jagorancinsa.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: An yi gobara a kasuwar ’yan gwan-gwan da ke Kano

Wata gobara da ta auku safiyar wannan Larabar ta laƙume kasuwar ’yan gwan-gwan da ke unguwar Dakata a Ƙaramar Hukumar Nassarawa ta Jihar Kano.

Kasuwar wadda ake kira da Kwalema tana nan a kan titin Zango, daura da gidajen man Dominion da kuma Mobil da ke makwabtaka da ofishin Hukumar WAEC.

Cire Gwamna Fubara ya saɓa wa Kundin Tsarin Mulki — Lauyoyi DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna

Mai magana da yawun hukumar kwana-kwana Saminu Yusuf Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa jami’ansu na ci gaba da ƙoƙarin kashe gobarar da ke neman wuce gona da iri.

Sai dai ya bayyana cewa duk da bincike ya soma gudana, amma kawo yanzu ba su gano musabbabin tashin gobarar ba.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An wawushe motar abinci ta Hukumar WFP a Borno
  • Sin Ta Mika Tallafin Wasu Jirage Marasa Matuka Na Inganta Noma Ga Kasar Zambia
  • Gwamnatin Nasarawa Ta Fara Aikin Sabunta Asibitoci 58 Don Inganta Lafiyar Jama’a
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina
  • Amurka ce Kadai Ta Ki Yin Allawadai Da Killace Gaza A Tsakanin Mambobin Kwamitin Tsaro na MDD
  • HOTUNA: An yi gobara a kasuwar ’yan gwan-gwan da ke Kano
  • WSCIJ Ta Naɗa Farfesa Umaru Pate A Kwamitin Amintattu
  • Waiwaye: Jihohin Da Aka Taɓa Sanya Dokar Ta-ɓaci A Nijeriya
  • Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Kwamishinan Ganduje Kan Zargin Ɓatan N240m