Leadership News Hausa:
2025-04-14@17:18:49 GMT

Xi Jinping Ya Yi Rangadi a Birnin Lijiang Na Lardin Yunnan

Published: 20th, March 2025 GMT

Xi Jinping Ya Yi Rangadi a Birnin Lijiang Na Lardin Yunnan

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi rangadi a birnin Lijiang na lardin Yunnan dake kudu maso yammacin kasar Sin da yammacin jiya, inda ya ziyarci lumbunan samar da furanni masu aiki da sabbin fasahohi na zamani da tsohon garin Lijiang, don fahimtar yadda ake raya aikin gona na musamman mai la’akari da yanayin wurin, da yadda ake gaggauta karewa da amfani da kayayyakin al’adu na tarihi da aiwatar da ra’ayin dunkulewar al’umomin Sinawa.

Lambun renon furanni mai aiki da fasahar zamani na Lijiang na da fadin hekta 73.3, wanda ya hada aikin shuka da sufurin furanni da yawon bude ido tare, kuma ya habaka aikinsa zuwa harhada man furanni da samar da busassun furanni da sarrafa abinci mai hade da furanni da sauransu. A kan yi jigilar kayayyakin da ya kan samar ba kadai zuwa manyan birane kamar Beijing da Shanghai da Guangzhou da sauransu ba, har da kai su kasashen waje kamar Japan da Vietnam da Rasha da sauransu, matakin da ya samar da karin guraben aikin yi kimanin 300 a kauyukan dake kewayensa.

Yayin ziyararsa, Xi Jinping ya ce, “ku gudanar da wannan aiki da kyau, wanda ya dace da alkiblar da ake bi na zamanatar da aikin gona. Ina fatan rayuwarku za ta yi kyau tamkar kyawawan furanni.”

Garin gargajiya na Lijiang na da tarihi fiye da shekaru 800. Shugaba Xi ya ce, al’adu da shimfidar wurin da hikimomin al’ummar wannan wuri na jawo hankalin mutane sosai, kuma haduwar al’adu da sha’anin yawon bude ido na ciyar da tattalin arzikin wuri gaba. Ya kara da cewa, ya kamata a raya wannan sha’ani bisa hanya mai kyau da dorewa. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?

Lamarin ya faru ne a lokacin da matashin mawakin yake kan dandamali ya na rera daya daya daga cikin fitattun wakokinsa, har zuwa lokacin wannan rahoto, Bilal Billa bai fitar da wata sanarwa a kafafen sadarwar ba, amma kuma faruwar lamarin ya janyo cece kuce inda wasu a bangare guda ke ganin abin da aka yi wa mawakan ya yi daidai yayin da wasu kuma ke ganin hakan bai dace ba.

Wasu na ganin cewar kalmar nan ta bahaushe da ya ce “Bokan Gida Bai Ci”, shi ne ke faruwa a kan wadannan mawakan, wasu kuma na ganin wannan wata hanya ce da aka dauko domin dakile tauraruwarsu da ke haskawa, wasu kuma ke cewa wannan kawai wata hanyar nuna hassada ce da mutanen arewacin Nijeriya ke amfani da ita saboda a kudancin kasar irin wannan ba kasafai yake faruwa tsakanin mawaka da sauran al’umma ba.

Ko ma dai minene dalilin da ya janyo jifar mawakan, ba zai rasa nasaba da banbancin ra’ayi ba kokuma rashin jituwa a tsakanin mawaka da masu saurarensu akan wani abinda su ka taba fafi ko aikatawa a cikin wakokinsu, sau da dama mawakan siyasa na fuskantar wannan kiyayya daga masoyansu wadanda ra’ayinsu ya saba a siyasance.

A wani lokaci can baya shahararren mawakin siyasa a Nijeriya Alhaji Dauda Adamu Kahutu wanda aka fi sani da Rarara ya fuskanci kalubale daga mutane da suke da banbancin ra’ayin siyasa, har ta kai ga wasu fusatattun matasa sun farmaki ofishinsa domin nuna fushi a kan wakokin suka ko tsangwama da yake yi wa gwaninsu a siyasance.

Amma kuma ba kasafai ake samun mawakan nanaye, nishadi ko soyayya da samun tsama tsakaninsu da masoyansu ba, duba da cewar mafi yawan lokutan mawakan kan sosa masu inda yake yi masu kaikayi a fagen soyayya, amma kuma wadannan al’amura da su ka faru a wannan shekarar ya jefa tambaya a zukatan wasu da dama a kan MI YA JANYO JIFAR MAWAKA A AREWACIN NIJERIYA.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” Na Harshen Vietnam
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
  • Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa
  • Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci
  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan