Leadership News Hausa:
2025-03-21@00:33:20 GMT

Xi Jinping Ya Yi Rangadi a Birnin Lijiang Na Lardin Yunnan

Published: 20th, March 2025 GMT

Xi Jinping Ya Yi Rangadi a Birnin Lijiang Na Lardin Yunnan

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi rangadi a birnin Lijiang na lardin Yunnan dake kudu maso yammacin kasar Sin da yammacin jiya, inda ya ziyarci lumbunan samar da furanni masu aiki da sabbin fasahohi na zamani da tsohon garin Lijiang, don fahimtar yadda ake raya aikin gona na musamman mai la’akari da yanayin wurin, da yadda ake gaggauta karewa da amfani da kayayyakin al’adu na tarihi da aiwatar da ra’ayin dunkulewar al’umomin Sinawa.

Lambun renon furanni mai aiki da fasahar zamani na Lijiang na da fadin hekta 73.3, wanda ya hada aikin shuka da sufurin furanni da yawon bude ido tare, kuma ya habaka aikinsa zuwa harhada man furanni da samar da busassun furanni da sarrafa abinci mai hade da furanni da sauransu. A kan yi jigilar kayayyakin da ya kan samar ba kadai zuwa manyan birane kamar Beijing da Shanghai da Guangzhou da sauransu ba, har da kai su kasashen waje kamar Japan da Vietnam da Rasha da sauransu, matakin da ya samar da karin guraben aikin yi kimanin 300 a kauyukan dake kewayensa.

Yayin ziyararsa, Xi Jinping ya ce, “ku gudanar da wannan aiki da kyau, wanda ya dace da alkiblar da ake bi na zamanatar da aikin gona. Ina fatan rayuwarku za ta yi kyau tamkar kyawawan furanni.”

Garin gargajiya na Lijiang na da tarihi fiye da shekaru 800. Shugaba Xi ya ce, al’adu da shimfidar wurin da hikimomin al’ummar wannan wuri na jawo hankalin mutane sosai, kuma haduwar al’adu da sha’anin yawon bude ido na ciyar da tattalin arzikin wuri gaba. Ya kara da cewa, ya kamata a raya wannan sha’ani bisa hanya mai kyau da dorewa. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sashen Masana’antun Dijital Na Kasar Sin Ya Samu Karin Riba Da Ci Gaba A Shekarar 2024

Alkaluma daga ma’aikatar masana’antu da fasahar sadarwa ta kasar Sin ko MIIT, sun nuna irin ci gaba bisa daidaito da sashen masana’antun dijital na kasar Sin ya samu a shekarar 2024 da ta gabata, inda a shekarar ta bara sashen ya samu karin kudin shiga da riba.

Alkaluman da MIIT ta fitar a jiya Litinin, sun nuna a baran, sashen ya kudin da ya kai kudin Sin yuan tiriliyan 35, kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 4.9, wanda hakan ya nuna karuwar kaso 5.5 bisa dari a shekara. Kazalika, jimillar ribar da sashen ya samar ta karu da kaso 3.5 bisa dari a shekara, inda ya kai yuan tiriliyan 2.7.

Bugu da kari, a shekarar ta 2024, karin kimar hajoji da manyan masana’antun kirar na’urori masu kwakwalwa ke samarwa, da na na’urorin sadarwa da sauran kayayyakin laturoni, ya karu da kaso 11.8 bisa dari, karin da ya kai na kaso 8.4 bisa dari kan na shekarar da ta gabace ta.

Fannin samar da manhajoji na kasar, shi ma ya samar da karin ribar kaso 10 bisa dari, inda darajarsa ta kai tiriliyan 13.7. Ana kuma danganta ci gaban fannin da fadadar sashen fasahohin kirkirarriyar basira ko AI, da dandalolin adana bayanai, da sauran sassan hada hadar kasuwanci masu alaka da shi. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Taimakon NAMA Don Gudanar Da Aikin Hajjin Bana Cikin Nasara 
  • Xi Ya Bukaci A Bude Sabbin Hanyoyin Samun Ci Gaba Yayin Rangadinsa A Lardin Yunnan
  • Gwamnatin Nasarawa Ta Fara Aikin Sabunta Asibitoci 58 Don Inganta Lafiyar Jama’a
  • Kungiyar Hamas Ta Ce Falasdinawa Ba Za Su Bar Kasarsu Ba, Ko Da Son Ransu Ko Da Karfi
  • Mutane Da Dama Ne Ake Jin Tsoron Sun Rasa Rayukansu A Lokacinda Motar Daukar Gas Ta Yi Bindiga A Kan Gadar Karu A Birnin Abuja
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [12]
  • Sabon Kawancen Jihohin Arewacin Najeriya Da Kamfanonin Sin Zai Fa’idantar
  • Wata Kungiya Mai Zaman Kanta Ta Samar Da Rijiyoyin Burtsatse A Karamar Hukumar Ringim
  • Sashen Masana’antun Dijital Na Kasar Sin Ya Samu Karin Riba Da Ci Gaba A Shekarar 2024