Hare-Haren Isra’ila Cikin Dare Sun Hallaka Mutum Aƙalla 50 A Gaza
Published: 20th, March 2025 GMT
Ƙungiyar bada agaji ta Civil defence a zirin Gaza ta ce hare-hare ta sama da Isra’ila ta kai cikin dare sun yi sanadin mutuwar mutum aƙalla 50 ciki harda yara ƙanana.
Hamas wadda zirin Gaza ke ƙarƙashin ikonta ta ce ta yi alla wadai da farmaki ta kasa na sojoji Isra’ila kuma ta bayyana shi a matsayin abinda ya saɓawa yajejeniyar tsagaita wuta na watanni biyu.
Rahotanni sun ce hare-haren da Isra’ila ta kai tun ranar Litinin wanda ya kawo ƙarshen yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta da Hamas, sun shafi wata makaranta da ake tsugunar da waɗanda suka rasa muhalansu.
Tun da farko Ministan tsaron Isra’ila, Isreal Katz ya gargaɗi almummar Gaza akan cewa za a lalata yankin bakiɗaya idan ba su dawo da waɗanda aka yi garkuwa da su ba tare da katse duk alaƙa da Hamas.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Yahudu
এছাড়াও পড়ুন:
Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno
Wasu karin majiyoyi sun nuna cewa, wannan hanyar ta hada Maiduguri da wasu kananan hukumomi da ke kudancin jihar Borno, wacce ta kasance yankin da yan ta’addan Boko Haram ke yawan kai hare-hare tsawon shekaru.
A baya hanyar, ta kasance a rufe amma Gwamnan jihar, Farfesa Babagana Zulum ya bude ta, domin bai wa jama’a damar ci gaba da zirga-zirga a yankin da suka hada da Damboa, Chibok da sauran kananan hukumomi a kudancin Borno tare da taimakon rakiyar sojoji a matsayin kariya.
An kwashe wadanda suka rasun tare da wadanda suka jikkata, wanda har yanzu ba a tantance adadinsu ba, zuwa asibiti a Maiduguri domin samun kulawar likitoci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp