Hare-Haren Isra’ila Cikin Dare Sun Hallaka Mutum Aƙalla 50 A Gaza
Published: 20th, March 2025 GMT
Ƙungiyar bada agaji ta Civil defence a zirin Gaza ta ce hare-hare ta sama da Isra’ila ta kai cikin dare sun yi sanadin mutuwar mutum aƙalla 50 ciki harda yara ƙanana.
Hamas wadda zirin Gaza ke ƙarƙashin ikonta ta ce ta yi alla wadai da farmaki ta kasa na sojoji Isra’ila kuma ta bayyana shi a matsayin abinda ya saɓawa yajejeniyar tsagaita wuta na watanni biyu.
Rahotanni sun ce hare-haren da Isra’ila ta kai tun ranar Litinin wanda ya kawo ƙarshen yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta da Hamas, sun shafi wata makaranta da ake tsugunar da waɗanda suka rasa muhalansu.
Tun da farko Ministan tsaron Isra’ila, Isreal Katz ya gargaɗi almummar Gaza akan cewa za a lalata yankin bakiɗaya idan ba su dawo da waɗanda aka yi garkuwa da su ba tare da katse duk alaƙa da Hamas.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Yahudu
এছাড়াও পড়ুন:
Gaza: Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sanadiyar Hare-Haren HKI Ya Dara 400
HKI ta keta yarjeniyar tsagaita wuta a Gaza, a jiya inda ta kai hare-hare masu yawa, wadanda suka yi sanadiyar mutuwar mutane fiye da 300 ya zuwa safiyar yau.
Tashar talanijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa, jiragen yakin HKI sun kai hare-haren a kan yankunan zirin Gaza da dama, kuma yawan mutanen da suka yi shahada ya zuwa yanzu ya kai 342 kumamafi yawansu mata da yara ne.
Labarin ya kara da cewa a garin Khan Yunus na kudancin Gaza jiragen yakin HKI sun kashe falasdinawa 77 sannan falasdinawa akalla 20 suka kashe a birnin Gaza. SAMA kamfanin dillancin labaran Falasdinawa ya bayyana cewa daruruwan Falasdinawa sun rasa rayukansu, kuma har yanzun ana neman wasu a wuraren da yahudawan suak kai hare hare.
Tashar talabijin ta Aljazeera ta bada labarin cewa hare-haren yahudawan sun game dukkan zirin gaza kuma sai da suka girgiza yanking aba daya.
Wasu masana suna ganin sojojin yahudawan sun yi amfani da sabbin makamai masu tun 20 wadanda gwamnatin Trump ta bawa HKI bayan ya dare kan kujerar shugabancin kasar ta Amurka.