Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu
Published: 20th, March 2025 GMT
Darakta mai kula da al-amuran mata da kuma kare hakkin bil’adama a ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran, Forouzandeh Vadiati, ta hadu da jakadan kasar Jamus a nan Tehran da kuma mataimakin jakadan kasar Burtania a Tehrana a ma’aikara. Inda ta bayyana masu bacin ranta da yadda kasashen biyu suka shigar da wata daftari ta tuhumar Iran da abinda ya shafi hakin mata da a hukumar kare hakkin bil’adama ta MDD.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Vadiati yana zargin Berlin da kuma London na shiga cikin al-amuran cikin gida na JMI. Sannan ta tunanatar da kasar Jamus kan abinda ta aikata na bawa Sadam Hussain makaman guba a yakin shekaru 8 da suka fafata da kasar ta Iraki.
Sannan ta bayyana yadda kasar Burtania ta dade tana adawa da JMI, daga ciki har da goyon bayan da kasashen biyu suke bawa HKI a kissan kiyashin da take wa falasdinawa a gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Hamas Ta Ce Falasdinawa Ba Za Su Bar Kasarsu Ba, Ko Da Son Ransu Ko Da Karfi
Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza ta bada sanarwan cewa mutanen Gaza ba za su taba barin kasarsu ba, da son ransu ko da karfi zuwa wani wuri ba, sai zuwa birnin Qudus babban birnin kasar Falasdinu.
Tashar talabijin ta Presstv ya nakalto kungiyar na fadar haka a jiya Laraba. Ta kuma kara da cewa duk abinda HKI da babbar kawarta Amurka zasu yi don fiddasu daga kasarsu ba zai kai ga nasara ba da yardar All…
Tun shekara 1948 ne kasar Burania a lokacin, wacce ta mamaye kasar Falasdinu ta mikawa yahudawan Sahyoniyya kasar Falasdinu, sannan suka kara mamayar kasar bayan yakin shekara 1967. Inda yahudawan suka mamaye har da gabacin birnin Qudus sannan sun ginawa yahudawa Sahyoniyya rukunan matsugunai har zuwa 12 a gabacin birnin Qudus.
Tun lokacin ne Falasdinawa suke gwagwarmaya don kawo karshen mamayar.
A yakin baya-bayan nan dai, wanda aka fara a cikin watan Octoban shekara ta 2023, yahudawan sun kashe falasdinawa kimani 48,000 a gaza kadai, don korar Falasdinawa daga yankin, amma bayan sun kasa korarsu sai aka tsagaita wuta tsakaninsu a cikin watan Jenerun wannan shekarar. Amma a makon da ya gabata yahudawan suka yi watsi da yarjeniyar suka koma yaki da nufin korarsu daga Gaza , a wannan karon tare da taimakon kai Amurka kai tsaye.