Majalisar wakilai ta amince da dokar ta-ɓaci a Ribas
Published: 20th, March 2025 GMT
Majalisar Wakilai ta amince da ayyana dokar ta-ɓaci da Shugaba Bola Tinubu ya yi a Jihar Ribas.
Majalisar ta yanke wannan shawara ne a ranar Alhamis, ta hanyar kaɗa ƙuri’a da baki, inda ’yan majalisa 243 suka halarta.
Muhimman ayyuka 8 a goman ƙarshe na Ramadan Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a AbujaA matsayin wani ɓangare na matakan dokar ta-ɓaci, majalisar ta bayar da shawarar kafa kwamiti domin dawo da zaman lafiya a jihar.
Hakazalika, majalisar za ta karɓi ragamar gudanar da ayyukan Majalisar Dokokin Jihar Ribas na tsawon watanni shida.
Me Ya Sa Aka Ayyana Dokar Ta-ɓaci?Matakin ya biyo bayan rikicin siyasa da ya ƙi ya ƙi cinyewa a Jihar Ribas.
Shugaba Tinubu ya yanke wannan shawara ne sakamakon tashe-tashen hankula da rikicin shugabanci a jihar.
Gwamna Siminalayi Fubara na takun-saƙa da Majalisar Dokokin Jihar da wasu jiga-jigan ’yan siyasa musamman waɗanda ke tsagin tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike, lamarin da ya jefa jihar cikin tashin hankali.
Domim shawo kan matsalar, Tinubu ya naɗa Tsohon Babban Hafsan Rundunar Sojin Ruwa, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), a matsayin sabon mai kula da jihar.
Hakan ya sa Gwamna Fubara da wasu manyan jami’ai, ciki har da iyalansa, suka bar gidan gwamnatin jihar.
Ana ci gaba da sa ido kan halin da ake ciki a jihar, yayin da gwamnati ke ƙoƙarin tabbatar da doka da oda a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Amincewa Dokar Ta Ɓaci Goyon Baya Majalisar Wakilai
এছাড়াও পড়ুন:
An kama miyagun kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
Jami’an tsaro sun kwace miyagun kwayoyi da kudinsu ya kai Naira miliyan 300 sannan ta kama mutane 650 da ake zargi a Jihar Kano.
Kwamitin Dawo da Zaman Lafiya da Kyautata Dabi’un Matasa ta Jihar Kano ce ta yi wanna kame a fadin jihar, kamar yadad ta bayyana a rahotonta.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Ibrahim Bakori, ya bayyana, ya bayana cewa mutum 150 daga ckin adadin an kama su ne kan laifukan dabanci da kwacen wayada da dangoginsu.
Kwamitin ya ce aikin haɗin gwiwar, ya yi wannan nasara ne bayan da suka kai samame a kan maboyar masu aikata laifuka da aka gano a kananan hukumomi takwas da ke garin Kano.
An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken TinubuHukumar ta bayyana cewa an gudanar da aikin ne tare da ’yan sanda da Hukumar Yaki da Miyagun Kwayoyi (NDLEA) da Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (NSCDC) da Hukumar Kula da Gidajen Yari da Hukumar Shige da Fice, da sauran hukumomi.
Da yake jawabi a wani taro da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro, Shugaban Rundunar, Dakta Yusuf Ibrahim, ya ce ƙwace miyagun ƙwayoyin da aka kiyasta kimarsu a Naira miliyan 300 zai taka muhimmiyar rawa.
Ya kuma jaddada muhimmiyar rawar da tallafin al’umma ke takawa wajen dorewar ƙoƙarin Rundunar na inganta tsaron jama’a.
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Aminu Abdussalam, ya yaba wa nasarorin da Rundunar ta samu, yana mai tabbatar da kudurin gwamnatin jihar na magance ƙalubalen tsaro ta hanyar irin waɗannan matakai masu ƙarfi. Sa’annan ya jaddada buƙatar haɗin gwiwa tsakanin hukumomi da al’umma don samun ɗorewar tsaro.
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano, ya yaba da ingancin ayyukan da aka gudanar bisa ga bayanan sirri, yana amai kira da a kafa wata kotu ta musamman domin hanzarta shari’ar waɗannan laifuka.
Kwamandan Hukumar NDLEA na Jihar, Abubakar Idris, ya yaba da haɗin gwiwar da ke tsakanin hukumomin tsaro kuma ya yi kira da a ci gaba da shidon magance matsalolin tsaro a Jihar Kano.