Rundunar ‘yansandan babban birnin tarayya Abuja ta tabbatar da mutuwar mutane shida a fashewar tankar man fetur da ya afku a yankin Karu da ke Abuja a daren Laraba. Rundunar ta kuma ce motoci 14 ne suka kone a mummunan hatsarin. Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan Gombe Kakakin rundunar ‘yansandan, SP Josephine Adeh, wanda ya bayyana hakan a ranar Alhamis, ya bayyana cewa, rundunar ta yi matukar jimamin hatsarin motar da ya afku a ranar 19 ga Maris, 2025, da misalin karfe 6:58 na yamma kafin gadar Nyanya.

Ta kuma ce, ofishin hukumar na Karu ya samu kiran gaggawa na faruwar lamarin, inda wata motar tirela ta Dangote, dauke da siminti da ta nufo gadar Nyanya daga AYA ta afka cikin motocin da ke tsaye cikin cunkoso.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Saura Kiris a Samin Tashin Gobarar Tankar Mai a Sakkwato

An dakile fashewar wata babbar tankar mai a Sokoto bayan da jami’an tsaro da jami’an kwana-kwana da masu bayar da agajin gaggawa suka yi gaggawar kai dauki bayan da tankar ta kife a hanyar Gagi-Nakasari a karamar hukumar Sokoto ta Kudu.

 

Wani shaidan gani da ido, Magaji Shanono ya shaidawa gidan rediyon Najeriya cewa tankar mai dauke da lita dubu arba’in da biyar na man fetur, ta wuntsila ne a lokacin da take kokarin shiga shatatalen Nakasari, inda ta zubar da mai.

 

Duk da cewa har zuwa lokacin hada wannan rahoto ba a fitar da wata sanarwa a hukumance ba, sakataren gwamnatin jihar Sokoto Muhammad Bello Sifawa ya halarci wurin da lamarin ya faru, domin ganin abin da ya faru.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Sokoto ya kuma sa ido kan matakan tsaro yayin da jami’an kashe gobara suka yi ta kokarin shawo kan lamarin.

 

Tawagar hadakar hukumar kashe gobara ta tarayya da ta jaha sun isa wurin da gaggawa, inda suka zuba kumfa don kawar da tururin wuta da hana tashin gobara a wajen.

 

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa NEMA da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar SEMA su ma sun wajen don shawo kan cunkoson jama’a, da kuma dakile hadurruka.

 

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa jami’an agajin gaggawa sun yi nasarar kwashe man zuwa wata tankar mai, inda suka kawar da illar zubewa ko fashewa.

 

Jami’an tsaro sun takaita zirga-zirga a wurin da lamarin ya faru, tare da hana mazauna wurin yunkurin diban mai.

 

NASIR MALALI

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane Fiye Da 30 Ne Suka Rasa Rayukansu A Lokacinda Motar Dawkar Gas Ta Yi Bindiga A Abuja Na Tarayyar Najeriya
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina
  • Saura Kiris a Samin Tashin Gobarar Tankar Mai a Sakkwato
  • Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a Abuja
  • Mutane Da Dama Ne Ake Jin Tsoron Sun Rasa Rayukansu A Lokacinda Motar Daukar Gas Ta Yi Bindiga A Kan Gadar Karu A Birnin Abuja
  • Da Ɗumi-ɗumi: Ana Fargabar Mutuwar Mutane Da Dama Yayin Da Tankar Mai Ta Fashe A Hanyar Zuwa Abuja 
  • Matatar Dangote Ta Dakatar Da Sayar Da Man Fetur A Naira
  • Harin Jirgin Yakin Sojoji Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 18 A Kasuwa
  • ‘Yansanda Sun Kama Wata Mata Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Katsina