’Yan Najeriya na iya fuskantar karin farashin man fetur bayan da Matatar Man Dangote ta bayyana cewa ta daina sayar wa ’yan kasuwa man fetur a kudin Naira.

Matatar, wacce ke siyan danyen mai da Naira bisa yarjejeniyar gwamnati, yanzu ta koma sayan danyen mai da dalar Amurka.

An kirkiro yarjejeniyar siyan danyen mai da Naira ne domin rage tsadar mai.

Bisa ga wannan yarjejeniya, Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL), yana da alhakin samar wa Matatar Dangote gangar danyen mai a kowace rana 385,000, domin ta tace ta kuma sayar da shi a farashin Naira.

Sai dai rashin cika alkawari daga NNPCL ya sa yarjejeniyar ta gaza dorewa.

Wata majiya ta bayyana cewa, “NNPCL bai cika alkawarin da ya dauka ba, hakan ya sa Dangote ba shi da wani zabi illa ya fara siyan danyen mai da dala.

“Yanzu matatun cikin gida sai sun samu dala kafin su iya ci gaba da aiki.”

Matatar Dangote ta ce, “Dole ne mu daidaita kudin sayar da kayayyakinmu da kudin da muke siyan danyen mai. Yarjejeniyar Naira ba ta samar da isasshen danyen mai da zai iya kula da aikinmu ba.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: siyan danyen mai

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun Qassam sun harba makami mai linzami a kan Tel Aviv

Dakarun Falasdinawa sun mayar da martani ga kisan kiyashin da Isra’ila ke yi wa fararen hula bayan sake dawo da yakin Isra’ila a kan al’ummar Gaza, inda suka harba rokoki zuwa Tel Aviv.

Al-Qassam Brigades, reshen soji na kungiyar gwagwarmayar Islama ta Hamas, ta sanar a wannan  Alhamis cewa, ta yi ruwan makamai masu linzami samfurin M90 a kan birnin Tel Aviv, a matsayin mayar da martani ga kisan kiyashi da Haramtacciyar Kasar Isra’ila ke yi kan fararen hula a zirin Gaza.

Sojojin mamaya na Isra’ila sun tabbatar da cewa sun gano wasu rokoki guda uku da aka harba daga Gaza zuwa tsakiyar Falasdinu da suka mamaye, tare da jin karar makamai a sararin samniyar Tel Aviv, Gush Dan, da matsugunan yahudawa da ke kewaye.

Isra’ila bat a mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta ba, kamar yadda ta yi fatali da mataki na biyu na yarjejeniyar , tare da sanya wasu sharudda da gangan domin matsin lamba a kan kungiyoyin  gwagwarmayar Falasdinu.

Isra’ila Ta sake sabunta kai hare-hare a zirin Gaza, inda ta kai hari a wurare daban-daban na yankin tun daga kwanaki biyu zuwa uku da suka gabata har zuwa yau.

Hare-haren na Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun yi sanadin shahadar daruruwan fararen hula, galibi mata da kanan yara, tare da jikkata wasu da dama .

Wakilin Al-Mayadeen ya tabbatar da cewa sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila sun sake raba arewacin Gaza daga tsakiya da kuma kudancin yankin, inda suka sake kwace iko da yankin Netzarim.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun Qassam sun harba makami mai linzami a kan Tel Aviv
  • Saura Kiris a Samin Tashin Gobarar Tankar Mai a Sakkwato
  • Farashin fetur na iya tashi bayan Dangote ya daina sayar da mai a Naira
  • Farashin fetur na iya tashi yayin da Dangote ya daina sayar da mai a Naira
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Wasu Teloli Cika Alƙawari
  • Matatar Dangote Ta Dakatar Da Sayar Da Man Fetur A Naira
  • Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira
  • Mutum 330 Sun Mutu Yayin da Isra’ila Ta Kai Wa Gaza Sabbin Hare-hare 
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Mai Karamin Karfi Zai Mallaki Muhalli Da Kudi Kalilan