OIC ta yi Allah wadai da sake dawo da hare-haren yahudawan sahyuniya a kan a zirin Gaza
Published: 20th, March 2025 GMT
Kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta duniya ta fitar da wata sanarwa inda ta yi Allah wadai da sake dawo da hare-haren wuce gona da irin da Isra’ila ke yi a zirin Gaza tare da yin kira da a dauki matakin gaggawa na kasashen duniya domin dakile wadannan laifuka.
Kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta yi Allah wadai da sake kai hare-haren bama-bamai a yankin zirin Gaza da yahudawan sahyuniya suka yi, lamarin da ya janyo hasarar rayukan fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Sheik Muhammad bin Abdulkarim Issa, babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta duniya, ya yi Allah wadai da zaluncin gwamnatin sahyoniyawa, wanda hakan ya saba wa dukkanin dokokin kasa da kasa.
Ya kuma jaddada bukatar daukar matakin gaggawa na kasashen duniya domin dakile wannan kisan kiyashi da mashinan yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare kan fararen hula da fararen hula.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yi Allah wadai da
এছাড়াও পড়ুন:
Dakarun Qassam sun harba makami mai linzami a kan Tel Aviv
Dakarun Falasdinawa sun mayar da martani ga kisan kiyashin da Isra’ila ke yi wa fararen hula bayan sake dawo da yakin Isra’ila a kan al’ummar Gaza, inda suka harba rokoki zuwa Tel Aviv.
Al-Qassam Brigades, reshen soji na kungiyar gwagwarmayar Islama ta Hamas, ta sanar a wannan Alhamis cewa, ta yi ruwan makamai masu linzami samfurin M90 a kan birnin Tel Aviv, a matsayin mayar da martani ga kisan kiyashi da Haramtacciyar Kasar Isra’ila ke yi kan fararen hula a zirin Gaza.
Sojojin mamaya na Isra’ila sun tabbatar da cewa sun gano wasu rokoki guda uku da aka harba daga Gaza zuwa tsakiyar Falasdinu da suka mamaye, tare da jin karar makamai a sararin samniyar Tel Aviv, Gush Dan, da matsugunan yahudawa da ke kewaye.
Isra’ila bat a mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta ba, kamar yadda ta yi fatali da mataki na biyu na yarjejeniyar , tare da sanya wasu sharudda da gangan domin matsin lamba a kan kungiyoyin gwagwarmayar Falasdinu.
Isra’ila Ta sake sabunta kai hare-hare a zirin Gaza, inda ta kai hari a wurare daban-daban na yankin tun daga kwanaki biyu zuwa uku da suka gabata har zuwa yau.
Hare-haren na Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun yi sanadin shahadar daruruwan fararen hula, galibi mata da kanan yara, tare da jikkata wasu da dama .
Wakilin Al-Mayadeen ya tabbatar da cewa sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila sun sake raba arewacin Gaza daga tsakiya da kuma kudancin yankin, inda suka sake kwace iko da yankin Netzarim.