Aminiya:
2025-04-13@05:27:22 GMT

‘Za a fara biyan Naira 77,000 ga masu yi wa ƙasa hidima daga Maris’

Published: 20th, March 2025 GMT

Masu yi wa ƙasa hidima (NYSC), za su fara jin daɗin sabon alawus ɗin gwamnatin tarayya na N77,000.00 wanda aka sake duba shi da za a fara biya daga watan Maris, 2025.

Babban Darakta Janar (DG) na NYSC, Birgediya Janar Olakunle Oluseye Nafiu ne ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga masu yi wa ƙasa hidima a babban birnin tarayya, a ofishin NYSC na shiyya ta 3 da ke Wuse Zone 3 Old Parade Ground a yankin Garki a ranar Alhamis.

Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas ya isa gidan gwamnati ’Yan Boko Haram 7 sun miƙa wuya ga sojojin MNJTF a Borno

Ya sanar da masu yi wa  ƙasar hidima cewa ma’aikatar kuɗi ta sanar da Hukumar NYSC cewa an shirya kuɗaɗen alawus ɗin don fara biya.

Ya bayyana cewa jinkirin aiwatar da sabon alawus ɗin ya biyo bayan rattaba hannu ne kan kasafin kuɗi na shekarar 2025.

Yayin da yake yabawa mambobin NYSC bisa kiyaye manufofin shugabannin da suka kafa NYSC ta hanyar samar da haɗin kan ƙasa, haɗe kai da ci gaban ƙasa, shugaban NYSC ya roƙe su da su yi amfani da ma’anar yadda aka rubuta taken waƙen NYSC.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Garki

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta laftawa Iran sabbin takunkumai gabanin tattaunawar Oman

Gwamnatin Washington ta sanar da kakabawa Iran sabbin takunkumai kan shirinta na nukiliya an zaman lafiya, a matakin da Amurka ke ganin shi ne kawai hanyar matsin lamba kan Iran domin ta mika wuya game da shirint ana nukiliya.

Takunkumin, wanda ma’aikatar baitul malin Amurka ta sanar a jiya Laraba, ya shafi hukumomi biyar da kuma wani mutum guda da ke Iran, saboda abin da sashen ya bayyana a matsayin goyon bayan shirin nukiliyar Iran.

Baitul malin na Amurka ya ce bangarorin da aka laftawa takunkumin na baya baya nan sun hada da Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran (AEOI) da ta karkashinta, Kamfanin Fasaha na Centrifuge na Iran.

Sakataren baitul malin kasar Scott Bessent ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa: Rikicin rikon sakainar kashi da Iran ke yi na kera makaman kare dangi ya kasance babbar barazana ga Amurka da kuma barazana ga zaman lafiyar yankin da kuma tsaron duniya.

Binciken da Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya ta yi a cibiyoyin Nukiliyar Iran ya musanta ikirarin Iran na neman makaman Nukiliya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji
  • NIMASA Za Ta Adana Wa Nijeriya Dala Biliyan 400 A Shekara Daga Cazar Kudaden Safarar Kaya
  • Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13
  • 2027: Masu Shirin Yin Kawance Na Duba Yiwuwar Zakulo Dan Takarar Da Zai Yi Wa’adi Daya
  • Waraka Daga Bashin Ketare
  • Gwamnatin Sakkwato na biyan mafi ƙarancin albashin N70,000 – NLC
  • Matatar Ɗangote ta rage farashin fetur zuwa N865
  • Yadda masu safarar ɗan Adam ke yaudarar mutane ta intanet
  • Amurka ta laftawa Iran sabbin takunkumai gabanin tattaunawar Oman