Aminiya:
2025-03-21@04:05:21 GMT

Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe

Published: 20th, March 2025 GMT

Wata gobara mai muni ta laƙume gidaje uku a unguwar New GRA, a birinn jihar Gombe, a ranar Laraba inda ta bar iyalai cikin rashin matsuguni tare da asarar dukiya ta miliyoyin Naira.

Waɗanda abin ya shafa sun koka kan rashin damar ceto komai daga kayan su, kuma yanzu haka suna neman tallafin gaggawa domin sake farfaɗowa daga wannan masifa.

‘Za a fara biyan Naira 77,000 ga masu yi wa ƙasa hidima daga Maris’ Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas ya isa gidan gwamnati

Gobarar wadda ta tashi da rana tsaka, ta yi saurin yaɗuwa zuwa gidaje uku, inda ta ƙone su kurmus.

Hukumomin yankin har zuwa yanzu ba su bayyana ainihin dalilin tashin gobarar ba, yayin da waɗanda abin ya shafa suke zaune ba tare da matsuguni ko abinci ko kayayyakin amfani na yau da kullum ba.

Malama Sakina, ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa, cikin kuka tana mai bayyana cewa,  “Mun rasa komai. Babu wanda ya taimaka mana lokacin da gobarar ta tashi. Muna buƙatar taimako, musamman daga gwamnati da masu taimakon jama’a, domin mu sake tsayuwa. Kowa ya san halin ƙunci da ake ciki yanzu.”

Wani wanda gobarar ta shafa, Yakubu Baba Gombe, ya bayyana damuwa kan jinkirin da jami’an kashe gobara suka yi wajen isowa wurin. inda ya ce, “Lokacin da suka iso, komai ya riga ya ƙone.”

Iyalan da abin ya shafa yanzu haka sun dogara ne ga taimakon al’umma don samun tallafi na gaggawa. A halin yanzu kuma, mazauna yankin suna kira ga hukumomi da su gudanar da bincike kan lamarin tare da ɗaukar matakan kariya daga aukuwar irin wannan gobarar a nan gaba.

Wakilinmu ya yi ƙoƙarin ya ji ta bakin hukumar kashe gobara kan wannan gobarar amma lamarin ya citura

Wannan iftila’i ya bar mutane cikin baƙin ciki, yayin da iyalai ke roƙon taimako domin sake gina rayuwarsu. Ƙoƙarin jin ta bakin jami’an kashe gobara bai yi nasara ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: tashin gobara da abin ya shafa

এছাড়াও পড়ুন:

Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan Gombe

Ya kuma nuna jin daɗinsa da irin nasarorin da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Kwamared Alhassan Yahayan, inda ya ce an ɗora ƙungiyar kan kyakkyawan turbar da ya kamata don ta ci gaba da taka rawar gani wajen bunƙasa aikin jarida a Nijeriya.

 

Yahaya ya jaddada cewa akwai kyakkyawar dangantaka tsakanin gwamnatin Jihar Gombe da ‘yan jarida, yana mai bada tabbacin cewa wannan kyakkyawar alaƙa da haɗin gwiwa za su kasance ginshiƙin gudanar da mulki a jihar.

 

“Mu a Jihar Gombe muna alfahari da daɗaɗɗiyar dangantakar da muka ƙulla da ‘yan jarida; ‘yan jarida abokan aikinmu ne masu ƙima a fagen kawo ci gaba, kuma muna ci gaba da jajircewa wajen ganin sun ci gaba da yin aiki a yanayin da zai bunƙasa sana’o’insu da ‘yancinsu,” inji Gwamna Inuwa Yahaya.

 

Ya kuma bada tabbacin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa gwiwa da NUJ da sauran ƙungiyoyin yaɗa labarai don ba su damar ci gaba da kuma gudanar da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen ankarar da gwamnati da wayar da kan jama’a.

 

Gwamna Inuwa ya ƙara da cewa, “Gudunmawar da kuka bayar na da matuƙar muhimmanci wajen inganta demokraɗiyya, da riƙon amana, da kuma shugabanci na gari a Nijeriya, muna godiya da irin rawar da kuke takawa wajen faɗakar da jama’a, da kare gaskiya, da kuma inganta manufofin gaskiya da adalci,” in ji Gwamna Inuwa Yahaya.

 

Ya kuma jaddada ƙudurin gwamnatin jihar na yin haɗin gwiwa mai ɗorewa da ‘yan jarida, inda ya jaddada muhimmancinsu wajen ci gaban Jihar Gombe dama Nijeriya baki ɗaya.

 

“Muna fatan ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarmu da NUJ, kuma muna da yaƙinin cewa, tare, za mu ci gaba da gina ƙasa mai wadata, zaman lafiya da ci gaba,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun Qassam sun harba makami mai linzami a kan Tel Aviv
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina
  • Gobara Ta Babbake Wani Shago A Jihar Kwara
  • Cutar Sankarau Ta Kashe Mutane 56 A Kebbi
  • Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan Gombe
  • Gobara ta kashe yara 3, ta jikkata 13 a Yobe
  • Ribas: Fubara Ya Fice Daga Gidan Gwamnati Yayin Da Sabon Shugaba Ke Shirin Karɓar Mulki
  • HOTUNA: An yi gobara a kasuwar ’yan gwan-gwan da ke Kano
  • DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna