Aminiya:
2025-03-21@15:57:48 GMT

’Yan adawa sun shirya ƙalubalantar Tinubu a zaɓen 2027 – Atiku

Published: 20th, March 2025 GMT

Tsohon mataimakin shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar ya bayyana cewa yanzu haka ’yan adawar siyasa a ƙasar nan a shirye suke su ƙalubalanci shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Tun bayan da ya sha kaye a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Atiku ya riƙa yin taro da ’yan adawa don neman karɓe mulki daga hannun jam’iyya mai ci.

Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas ya isa gidan gwamnati

Da yake jawabi ga manema labarai tare da wasu ’yan adawa a zauren taro na ‘Yar’adua Center da ke Abuja a ranar Alhamis, Atiku ya ce an yi taron ne don sake samar da wasu ‘yan adawa kafin babban zaɓe mai zuwa.

Da yake amsa tambayoyi kan ko taron manema labarai na ƙawancen ‘yan adawa na nuni da haɗuwar jiga-jigan ‘yan adawa? Atiku ya ce, “Wannan ita ce samar da haɗakar ‘yan adawa gabanin 2027”.

A ranar Talata ne shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas, inda ya kori gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa da ’yan majalisar dokokin jihar, lamarin da ya sa ’yan adawa suka mayar da martani.

Da yake jawabi ga manema labarai a madadin shugabannin adawa a a zauren taron a Abuja, ranar Alhamis Atiku ya zargi Tinubu da son zuciya.

Sauran jiga-jigan ’yan adawa da suka halarci taron manema labarai sun haɗa da: Tsohon Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, wanda Yunusa Tanko ya wakilta, tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal, tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, sakataren haɗakar jam’iyyun siyasa na ƙasa, Peter Ameh, da dai sauransu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Atiku Abubakar Babachir Lawal manema labarai

এছাড়াও পড়ুন:

Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a Abuja

Asibitin Ƙasa da Asibitin Asokoro da ke Abuja sun cika maƙil da mutanen da suka jikkata sakamakon fashewar tankar gas da ta auku da daren Laraba a gadar Karu.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:14 na dare, bayan wata babbar mota ɗauke da gas ta yi hatsari, tare da faɗawa kan wasu motoci da ke kan gadar, lamarin da ya haddasa gobara.

Sarakunan Kano su kimtsa wa hawan sallah bana — Abba Fubara ya magantu bayan ayyana dokar ta ɓaci a Ribas

Rahotanni sun nuna cewa an rasa rayuka da dama, yayin da mutane da yawa suka samu munanan raunuka.

Shugaban Sashen Ɗaukar Matakan Gaggawa na Hukumar Kula da Harkokin Gaggawa ta Ƙasa (FEMA), Mista Mark Nyam, ya bayyana cewa jami’an hukumar sun isa wajen domin ceto mutanen da abin ya shafa.

Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya da ta Babban Birnin Tarayya, ’Yan Sanda, da Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) sun duƙufa wajen kai ɗauki.

Wasu daga cikin waɗanda suka jikkata an kai su Asibitin Fadar Shugaban Ƙasa domin samun kulawar gaggawa.

Shirin Inganta Amfani da Gas (PCNG) na Fadar Shugaban Ƙasa, ya bayyana jimaminsa game da wannan hatsari.

Ya yi alƙawarin gudanar da bincike don gano musabbabin aukuwar lamarin.

Rahotanni sun nuna cewa tankar gas ɗin ta samu matsalar birki, wanda hakan ya haddasa fashewar tankin mai.

A cikin wata sanarwa, PCNG ya buƙaci jama’a da su guji yaɗa jita-jita har sai an kammala bincike.

Hakazalika, ya jaddada aniyarsa na tabbatar da aminci wajen amfani da CNG, tare da ɗaukar matakan hana aukuwar irin wannan hatsari a nan gaba.

Jami’an agaji sun ci gaba da aikin ceto da bayar da taimako ga waɗanda lamarin ya shafa, tare da ƙoƙarin shawo kan ɓarnar da gobarar ta haifar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Zama Ƴar Amshin Shata — Kwankwaso
  • IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya
  • Babu ’yan adawan da za su iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027 — Ganduje
  • Mun Yi Watsi Da Ayyana Dokar Ta-Ɓaci Da Tinubu Ya Yi A Ribas – Shugabannin Adawa
  • Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a Abuja
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Gwamnan Rikon Kwarya Na Jihar Rivers
  • Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas
  • Atiku Ya Soki Tinubu Kan Ayyana Dokar Ta-ɓaci a Jihar Ribas
  • Shugaba Tinubu Ya Dakatar Da Gwamnan Jihar Rivers Da ‘Yan Majalisar Dokokin Jihar