Aminiya:
2025-04-13@04:59:19 GMT

’Yan adawa sun shirya ƙalubalantar Tinubu a zaɓen 2027 – Atiku

Published: 20th, March 2025 GMT

Tsohon mataimakin shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar ya bayyana cewa yanzu haka ’yan adawar siyasa a ƙasar nan a shirye suke su ƙalubalanci shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Tun bayan da ya sha kaye a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Atiku ya riƙa yin taro da ’yan adawa don neman karɓe mulki daga hannun jam’iyya mai ci.

Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas ya isa gidan gwamnati

Da yake jawabi ga manema labarai tare da wasu ’yan adawa a zauren taro na ‘Yar’adua Center da ke Abuja a ranar Alhamis, Atiku ya ce an yi taron ne don sake samar da wasu ‘yan adawa kafin babban zaɓe mai zuwa.

Da yake amsa tambayoyi kan ko taron manema labarai na ƙawancen ‘yan adawa na nuni da haɗuwar jiga-jigan ‘yan adawa? Atiku ya ce, “Wannan ita ce samar da haɗakar ‘yan adawa gabanin 2027”.

A ranar Talata ne shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas, inda ya kori gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa da ’yan majalisar dokokin jihar, lamarin da ya sa ’yan adawa suka mayar da martani.

Da yake jawabi ga manema labarai a madadin shugabannin adawa a a zauren taron a Abuja, ranar Alhamis Atiku ya zargi Tinubu da son zuciya.

Sauran jiga-jigan ’yan adawa da suka halarci taron manema labarai sun haɗa da: Tsohon Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, wanda Yunusa Tanko ya wakilta, tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal, tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, sakataren haɗakar jam’iyyun siyasa na ƙasa, Peter Ameh, da dai sauransu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Atiku Abubakar Babachir Lawal manema labarai

এছাড়াও পড়ুন:

Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba —Ganduje

Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi watsi da damuwar da ake nunawa kan ziyarar da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya kai wa tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, inda ya ce APC ba ta girgiza ba, kuma ta mayar da hankali ne kan karfafa madafunta.

A cikin wani bidiyo, a lokacin da yake yi wa manema labarai jawabi jim kadan bayan ya jagoranci masu ruwa da tsaki na APC zuwa ganawa da Buhari a gidansa, Ganduje ya ce sun ziyarci Buhari ne don sanar da shi irin nasarorin ci da jam’iyyar ta samu tun bayan barinsa mulki da kuma tabbatar da kudirinsu na tabbatar da ci-gaban ayyukansa.

“Ba mu ba damu ko kadan. Mun zo ne don girmama tsohon shugaban kasa kuma mu sanar da shi nasarorin da babbar jam’iyyarmu ta samu tun bayan saukarsa daga mulki. Mun tabbatar masa da cewa za mu ci gaba da sanar da shi ina aka kwana akai-akai game da halin da ake ciki,” in ji Ganduje.

Game da ziyarar Atiku ga Buhari, wadda ake gani a matsayin yiwuwar haɗewarsu a siyasa, Ganduje ya yi watsi da ita a matsayin mara muhimmanci.

“Wannan ziyarar ba ta dame mu ba. Ƙoƙari ne maimaita tarihi amma abin da suke nema ba zai yiwu ba. Abin da suke kokarin ginawa ba shi da tushe. Wasu ɓangarorin ba za su taɓa iya haɗuwa ba,” in ji shi.

Ko da yake ya ki yin ƙarin bayani, Amma ya yi nuni da cewa a shirye APC take don dakile duk wani yunkurin ’yan adawa, ko da yake bai yi ƙarin bayani ba.

Ganduje ya ce, “Ba za mu bayyana shirinmu ba, amma mun riga mun shirya musu. Nasarorin da Shugaba Tinubu ya samu yana ƙara karfafa jam’iyyar,” in ji shi.

Ganduje ya kuma jaddada burin APC na karɓe fiye da jihohi 21 da take mulki a halin yanzu, yana mai bayyana ƙwarin gwiwa cewa jam’iyyar za ta samu karin jihohi ta hanyar sauya sheka ko zaɓe mai zuwa.

“Wasu gwamnoni za su iya dawowa cikinmu, ko kuma mu kayar da su a zaɓe. Ko ma mene ne dai, muna faɗaɗa mulkinmu. Muna gamsu da inda muke, amma ba za mu tsaya a iya nan ba.”

Da yake tsokaci kan sauya shekar da wasu kusoshin APC suka yi a kwanan nan da kuma rikicin cikin gida na jam’iyyar, Ganduje ya tabbatar da cewa tafiyarsu ba ta da wani tasiri mai yawa.

“Manyan mutane daga wasu jam’iyyu suna dawowa APC. ’Yan ƙalilan da suka tafi kuma babu wata illa ta a-zo-a-gani da za sai yi,” in ji shi.

Dangane da sukar da ake yi kan zargin gwmanatin Tinubu da nuna bangaranci a rabon muƙamai, Ganduje ya dage cewa ana raba mukamai daidai kuma jam’iyyar na tattara bayanai don tabbatar da adalci.

Ya ce, “Muna tara alƙaluman nadin mukamai don nuna cewa babu nuna bambanci a nadin mukaman shugaban kasa,” in ji shi.

Kalaman Ganduje na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da cukumurdar siyasa gabanin babban zaben 2027, inda jam’iyyun masu mulki da na adawa ke neman karfafa kawance da kuma sake dabaru.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Da Sifaniya Sun Daga Matsayin Hadin Gwiwa A Fannin Shirya Fina-finai
  • Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba —Ganduje
  • 2027: Masu Shirin Yin Kawance Na Duba Yiwuwar Zakulo Dan Takarar Da Zai Yi Wa’adi Daya
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Ba Matan Arewa Ta Gabas Su Dubu Tallafin Naira Miliyan 50
  • Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 17: Tinubu Ya Kare Yadda Gwamnatinsa Ke Tafiyar Da Tsarin Rabon Arzikin Kasa
  • Za a mayar da tubabbun ’Yan Boko Haram cikin al’umma – Gwamna Buni
  • Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki a NUPRC — Buba Galadima
  • Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki NUPRC — Buba Galadima
  • Malaman Makarantun Firamare 1,800 Sun Samu Horo Aka A Kwara