Aminiya:
2025-04-13@05:38:42 GMT

An wawushe motar abinci ta Hukumar WFP a Borno

Published: 20th, March 2025 GMT

Wasu da ba a san ko su wanene ba sun yi awan gaba da kayayyakin wata mota ɗauke da kayan abinci na Hukumar abinci ta duniya (WFP) a garin Gubio, yayin da take kan hanyarta ta zuwa Damasak a Jihar Borno.

Majiyar leƙen asiri ta shaidawa Zagazola Makama cewa, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:30 na rana lokacin da Aminu Malam Umar direban wata babbar mota ƙirar Iɓeco ya tsaya a gefen titi.

’Yan adawa sun shirya ƙalubalantar Tinubu a zaɓen 2027 – Atiku Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe

Yayin da motar ta tsaya a gefen titi ba tare da kula daga jami’an tsaro ba, wasu da ba a san ko su waye ba suka sace buhunan shinkafa da gishiri da sukari da wake da kuma man girki da dama, duk da cewa ba a tantance adadin da kuma darajar kayayyakin da aka sace ba har ya zuwa yanzu.

Jami’an tsaro sun ziyarci wurin da lamarin ya faru, amma ba a kama kowa ba.

Daga bisani sojoji sun ɗauke motar zuwa  Gubio lafiya lau a yayin da ake ci gaba da bincike don gano waɗanda suka aikata laifin tare da ƙwato kayayyakin da aka sace.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An Sace Dalibin Jami’ar Tarayya Birnin Kebbi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi, ta tabbatar da sace wani dalibi dan aji 4 na Jami’ar Tarayya ta Birnin Kebbi, mai suna Augustine Madubiya, mai shekaru 23 da haihuwa, wanda ke Sashen Tattalin Arziki zuwa inda ba a san inda aka nufa ba.

 

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar, ya shaida wa manema labarai cewa, wasu gungun ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kai farmaki gidan Istijaba Villa da ke karamar hukumar Kalgo a jihar inda suka yi garkuwa da wani dalibi a dakin kwanan dalibai a harabar jami’ar, kuma abin bakin ciki, wani Malam Siddi Hussaini, wanda ke kusa yana kiwon shanun sa, a lokacin da yake kokarin shiga tsakani, shi ma likita ya samu rauni a harin.

 

A cewarsa, yayin da yake samun rahoton, jami’in ‘yan sanda na yankin, Kalgo, ya tara tawagar jami’an tsaro hadin gwiwa zuwa wurin da lamarin ya faru, kuma a halin yanzu rundunar jami’an tsaro na ci gaba da sintiri dazuzzuka da kuma hanyoyin da ke kusa da wurin da nufin ceto wanda aka yi garkuwa da shi ba tare da jin rauni ba tare da damke wadanda suka aikata wannan ta’asa.

 

Hakazalika, a ranar Lahadin da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne na Lakurawa da ke dauke da manyan muggan makamai suka kai farmaki kauyukan Tungan Taura da Tungan Ladan, a karamar hukumar Augie a jihar Kebbi, inda suka yi awon gaba da wasu shanu da ba a tantance adadinsu ba, suka kashe mutum goma sha shida.

 

SP Nafiu Abubakar ya ce, tun daga lokacin an dawo da zaman lafiya a yankunan da lamarin ya shafa kuma an fara gudanar da cikakken bincike.

 

Abdullahi Tukur

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno
  • An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato
  • An saki fasto an kuma tsare wanda ya kai kuɗin fansa
  • Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto
  • ’Yan bindiga sun harbi alkali da ɗansa, sun sace mutane 13 a Katsina
  • Hisbah ta warware rigingimu 565 da lalata katan 51 na barasa a Yobe
  • Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta
  • Ruwa Ya Ci Rayukan Mata Biyu A Kano
  • An Sace Dalibin Jami’ar Tarayya Birnin Kebbi