Leadership News Hausa:
2025-03-21@19:17:47 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [13]

Published: 21st, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [13]

Ibnu Juzai al-Kalbi Allah Ya yi masa ranama yan nuna mana munin hassada ta fuska biyu:

1. A Ɗabi’a: Hassada tana haifar da cutar zuciya, wadda ke hana mutum farin ciki da jin daɗin rayuwa, kuma tana sa mai yin ta ya zama mai mugun hali, da ƙoƙarin ganin wani ya faɗi ko ya rasa abin da ya samu. A al’ada, mutane suna ƙin mai hassada saboda halayensa na rashin son alheri ga mutane da kuma fatan sharri a gare su.

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [12] Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]

2. A Shari’a: A cikin Alƙur’ani, Allah ya yi umurni da a nemi tsari a wurinsa daga hassadar mahassadi, inda Ya ce:” Ka ce:” Ina neman tsari da Ubangijin asuba. Daga sharrin abin da Ya halitta. Da kuma sharrin dare idan ya lulluɓe da duhu. Da kuma sharrin mata masu tofi a cikin ƙulle-ƙulle. Da kumma sharrin mahassadi yayin da ya yi hassada.” Suratul Falaƙ aya ta 1-5. Manzon Allah (ﷺ) ya ce: “Kada ku yi hassada da juna…” Muslim ne ya ruwaito [#2563].

Hassada tana iya kai mutum ga saɓawa Allah, kamar yadda Shaiɗan ya ƙi yin sujada ga Adam saboda kishi da hassada. Hassada tana haifar da cin amanar ‘yan’uwa, da munafunci, da karya. Hassada tana cutar da mai yin ta fiye da wanda ake yi wa. A ɗabi’a, tana hana kwanciyar hankali, a shari’a kuwa tana kai mutum ga zunubi. Maimakon yin hassada, Musulumi ya kamata ya roƙi Allah ya ba shi alheri kamar yadda Ya ba wa waninsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A karshe dai abin da wasu ke hasashen zai faru a Jihar Ribas ne ya faru inda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya saka dokar ta baci a jihar kuma ya dakatar da zababben gwamnan da mataimakiyarsa da kuma ’yan majalisar dokokin jihar.

Sai dai bayan wannan doka da shugaban kasar ya ayyana ne al’umma da dama ke ta bayyana mabanbantan ra’ayoyin kan wannan batu.

A yayin da wasu ke bayyana cewa dama tuni abin da shugaban kasar yake bukata ke nan, wasu kuwa ke bayyana cewa shugaban kasar ma ba shi da ikon dakatar da zababben gwamna.

NAJERIYA A YAU: Yadda Mai Karamin Karfi Zai Mallaki Muhalli Da Kudi Kalilan DAGA LARABA: Asalin Tashe Da Tarihinsa A Ƙasar Hausa?

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba ne kan shin ko Dokar Kasa ta bai wa shugaban kasa karfin ikon dakatar da gwamnan jiha dama ’yan majalisar dokokin ta?

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu
  • Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban Miyetti Allah A Filato
  • OIC ta yi Allah wadai da sake dawo da hare-haren yahudawan sahyuniya a kan a zirin Gaza
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [12]
  • Goman Ƙarshe: Dama ta ƙarshe ga mai neman rahamar Allah
  • Wakilin Sin Ya Yi Allah Wadai Kan Sabon Yaki Da Isra’ila Ta Tayar A Zirin Gaza
  • DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]