Aminiya:
2025-04-13@04:59:19 GMT

MAGGI: Girke-girken Ramadan masu kawo sauyi da zumunta

Published: 21st, March 2025 GMT

Ramadan lokaci ne da ke hada kan iyalai da al’ummomi a fadin duniyar Musulmi. Lokaci ne da masoya ke haduwa tun daga lokacin sahur har zuwa buda-baki, ta hanyar kasancewa tare domin cin abinci mai gina jiki.

A wannan lokacin, ba a yin abinci don nishadi kawai, lokaci ne na inganta rayuwa da bayar da labarai na nishadantarwa da zumunta da kuma jin dadin kasancewa tare.

A cikin wannan labari mai ban sha’awa na MAGGI mai taken Labarin Ramadan, wasu mata biyar sun yi tafiya ta tsawon wata guda don samar da sauye-sauye, inda suka gano hadaddun girke-girke na sada zumunta da ke da alaka da samar da labarai masu jan hankali, har guda shida.

Tare da wasu jaruman wasan kwaikwayo da suka hada da Rekiya Attah, Labaran MAGGI na Ramadan suna kunshe da labarai masu kayatarwa, kuma masu dadi har na tsawon mako shida da aka fara tun farkon wannan watan na Ramadan. Wannan yanayi ya zame wa kowa jiki, to amma ya fi dadi a yayin da muka hadu a matsayinmu na iyali ko al’umma a lokacin Ramadan.

Kowane bangare na labarin yana nuna ainihin yadda lokacin Ramadana yake, ta fuskar son juna da zumunci da kuma yadda ake samun gamsuwa a lokacin buda-baki. Ta fuskar lokutan fahimtar juna da ba a yi tsammani ba ake yaukaka dangantaka da tabbatar da cewa, abokantaka tamkar tsintsiya ce madaurinink daya, inda take kawo kwanciyar hankali da annashuwa har ma a lokutan da ake cikin tsanani.

Da take magana a kan kudirin MAGGI na karfafa danganta da abokan huldasa a lokacin Ramadan tsawon shekara goma da suka gabata, Manajan Girki ta Kamfanin Nestlé Nigeria, Misis Rahamatou Palm-Zakari ta ce, “Ramadan lakaci ne na kyauta da soyayya, wanda MAGGI yake jaddadawa. Ta hanyar ci gaba da gabatar da samfuran da girke-girkenmu masu farin jini da samar da labaran Ramdan a yanzu, mun sadaukar da kanmu wajen ci gaba da yin kyakkyawan tasiri a rayuwar abokan huldarmu. Ta hanyar kayayyakin da muke samarwa da dandadon girki, za mu ci gaba da tallafa wa daidaikun mutane da iyalai wajen zabin abinci mai dandano da kara lafiya a kowace rana.

A matsayin kamfani da ya kudiri aniyar hada kan mutane ta hanyar abinci, MAGGI ya yi imani da muhimmancin burin samun abinci mai dandano.

MAGGI wani bangare ne na Kamfanin Nestlé, wanda kamfani da yake samar da abinci mai dandano da kyakkyawar rayuwa da ya kudiri aniyar bayyana irin rawar da abinci yake takawa wajen inganta rayuwa kowa da kowa a yanzu da kuma zamani mai zuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Maggi Tales of Ramadan Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Yaɗa Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya

Idris ya gode wa kamfanonin Faransa da suka daɗe suna aiki a Nijeriya, irin su TotalEnergies, Lafarge, Peugeot, Danone, Alstom, Schneider Electric da sauran su, saboda gudunmawar da suke bayarwa a sassa daban-daban na ƙasar nan kamar makamashi, ababen more rayuwa, noma, lafiya da masana’antu.

 

Idris ya ce a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Nijeriya tana kan “tafarkin sauyi da ba a taɓa ganin irin sa ba” wanda Ajandar Sabunta Fata ke ɗauke da shi.

 

Ya ce: “Waɗannan sauye-sauyen tarihi na gina tattalin arzikin da ya fi gasa, mai gaskiya da amfanar masu zuba jari, suna mayar da Nijeriya ƙofar shiga kasuwar masu saye ta Afirka wadda ke bunƙasa, ƙarƙashin Yankin Ciniki Cikin ’Yanci na Nahiyar Afirka (AfCFTA).”

 

Wasu daga cikin sauye-sauyen da ya yi nuni da su sun haɗa da:

 

Daidaita tsarin musayar kuɗi, cire tallafin mai domin daƙile asara, tsarin farashin wutar lantarki da ya dace domin ɗorewar sabis.

 

Sauran sun haɗa da sauye-sauyen haraji da ke inganta gaskiya da sauƙaƙe kasuwanci, sababbin dokoki da tsare-tsaren kuɗi da ke ba da goyon baya ga masu zaman kan su, sauƙaƙe harkokin shigo da kaya ta hanyar National Single Window, da sauye-sauyen dijital ciki har da tsare-tsaren shige da fice.

 

Ministan ya ce Nijeriya tana da fa’ida ta musamman ga masu zuba jari: ita ce mafi girman tattalin arziki a Afirka, yawan jama’a fiye da miliyan 220 — fiye da kashi 70 nasu kuma matasa ne ‘yan ƙasa da shekaru 35 — da kuma shekaru sama da 26 na dimokiraɗiyya ba tare da katsewa ba.

 

Ya ƙara da cewa gwamnati tana tabbatar da cewa tattalin arzikin ƙasar yana gudana ne ƙarƙashin ƙa’idojin doka, tare da tallafin hukumomin da suka haɗa da CBN, NIPC, SEC, da FCCPC.

 

Ministan ya ce a cikin watanni 20 kacal da gwamnatin Tinubu, an sauya tsarin kuɗi na ƙasa, inda aka samu ƙaruwa da kashi 3.84 na GDP a zangon farko na shekarar 2024, da samun ƙarin kuɗin shiga fiye da kashi 20, tare da rage yawan kuɗin da ake kashewa wajen biyan bashi.

 

Ya ce: “Gwamnatin ta kasance mai ƙarfafawa wajen haɓaka sashen masu zaman kan su ta hanyar wasu muhimman shirye-shirye kamar Asusun Raya Ababen More Rayuwa na Sabunta Fata (RHIDF), Hukumar Bai wa Jama’a Lamunin Kaya ta Nijeriya (CrediCorp), Shirin Fadar Shugaban Ƙasa na CNG, Asusun Zuba Jari na Gidaje na MOFI (MREIF), da wasu da dama.

 

“Waɗannan shirye-shiryen suna shimfiɗa tubalin da za a iya dogaro da shi wajen jawo zuba jari na tiriliyan-triliyan na naira daga sashen masu zaman kan su a fannonin ababen more rayuwa, lamunin kayan masarufi, kiwon lafiya, gidaje, da sauran su.”

 

Ya kuma bayyana cewa bankunan Nijeriya suna ƙara faɗaɗa zuwa Turai, ciki har da buɗe ofisoshi a birnin Paris, yana mai cewa Nijeriya za ta ƙara samun wakilci a Faransa ta fannoni kamar ƙere-ƙere, fasaha da yaɗa labarai.

 

Ya gayyaci kamfanonin Faransa — musamman masu sha’awar harkar noma — da su ci gajiyar sababbin damarmakin da ke akwai a sashen kiwon dabbobi na Nijeriya, inda sabuwar Ma’aikatar Raya Kiwon Dabbobi ta buɗe ƙofofin sababbin haɗin gwiwa.

 

Ya ce: “Dole ne mu shirya wa gaba da ƙwazo da fata mai kyau, tare da ƙarfin gwiwar da kakannin mu suka nuna.”

 

A yayin zaman sa a Paris, Minista Idris zai gana da manyan hukumomin yaɗa labarai da al’adu na Faransa, kamar France Médias Monde, ARCOM, Ma’aikatar Al’adu, da Thomson Broadcast, domin ƙarfafa dangantaka tsakanin Faransa da Nijeriya a fannin watsa shirye-shirye da yaɗa labarai.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
  • Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji
  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan
  • 2027: Masu Shirin Yin Kawance Na Duba Yiwuwar Zakulo Dan Takarar Da Zai Yi Wa’adi Daya
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
  • Yunkurin Matasan Nijeriya Na Son Zama Attajirai A Dare Daya Ta Hanyar Caca
  • Sojojin Sama Na HKI Kimani 1000 Guda New Suka Bukaci A Kawo Karshen Yaki A Gaza
  • Tarkon Mutuwa a Katsina: Hanyar Funtua zuwa Ƙanƙara