Aminiya:
2025-04-14@07:07:11 GMT

Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas

Published: 21st, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi caccaki Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas.

Kwankwaso ya ce matakin da Tinubu ya ɗauka ya saɓa doka kuma barazana ne ga dimokuraɗiyya.

Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe NAJERIYA A YAU: Illar Sare Itatuwa Ga Sauyin Yanayi Da Lafiyarmu

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Kwankwaso ya gargaɗi cewa irin wannan matakin na iya kafa mummunan misali da kuma illata dimokuraɗiyya a Najeriya.

Kwankwaso, ya ruwaito yadda rikicin siyasa da ya haifar da soke zaɓen 1993, inda ya jaddada cewa ‘yan majalisa su daina ɓata lokacinsu kan abubuwan da ba su dace ba.

“Majalisa tana da alhakin sa ido kan ayyukan ɓangaren zartarwa, ba wai kawai yarda da duk abin da ta ce ba.

“Abu ne mai matuƙar tayar da hankali ganin yadda Majalisar Tarayya ta 10 ta fi kowace zama ‘yar amshin shata ga ɓangaren zartarwa,” in ji shi.

Tsohon gwamnan ya kuma soki yadda Majalisar Tarayya ta gaggauta amincewa da matakin Shugaba Tinubu ba tare da bin ƙa’idojin da kundin tsarin mulki ya tanada ba.

“Kundin tsarin mulki ya fayyace yadda ake yanke hukunci kan irin wannan matsala, amma ‘yan majalisa sun zaɓi amfani da murya wajen zaɓe, wanda hakan yana janyo shakku kan sahihancin lamarin.

“Gaggawar amincewa da dokar ta-ɓaci da zata kifar da gwamnatin da aka zaɓa, cin fuska ne ga dimokuraɗiyya,” in ji shi.

Kwankwaso ya kuma yi gargaɗi kan shigar sojoji cikin harkokin mulki, inda ya bayyana cewa hakan tamkar komawa baya ne bayan ci gaban da aka samu tsawon shekaru 26 na dimokuraɗiyya.

Ya bayyana damuwarsa cewa wannan matakin na iya zama wata dabara ta murƙushe jihohin da ba sa tare da jam’iyya mai mulki.

“A matsayinsa na wanda ke da’awar kare dimokuraɗiyya, Shugaba Tinubu ya kamata ya fi kowa fahimta cewa kawo sojoji cikin mulki hatsari ne.

“Wannan matakin ba wai kawai barazana ne ga zaman lafiya ba, yana iya zama hanyar kama-karya idan ba a dakatar da shi ba,” in ji Kwankwaso.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Kwankwaso Kwankwaso ya

এছাড়াও পড়ুন:

Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Sama Da 240 A Kebbi

Sama da gidaje dari biyu da arba’in ne aka lalata a daren Talatar da ta gabata, ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka shafe sa’o’i ana yi a unguwar Garin Kestu Atuwo dake karamar hukumar Shanga ta jihar Kebbi.

 

Da yake jajantawa wadanda abin ya shafa, Gwamna Nasir Idris ya shawarci gidajen da abin ya shafa da su dauki lamarin a matsayin wani kaddara daga Allah Ta’ala.

 

Shugaban karamar hukumar Shanga, Alhaji Audu Dan Audu, ya wakilce shi, ya ce ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi a daren ranar Talata ya lalata gidaje da dukiyoyi na miliyoyin Naira, ya kuma yi godiya ga Allah Madaukakin Sarki ganin yadda ba a yi asarar rayuka ba.

 

Ya kuma yi kira gare su da su yi hakuri domin nan bada jimawa gwamnatin jihar za ta mika musu tallafi da suka hada da kayayyakin gini.

 

Abdullahi Tukur

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Dakatar Da Matakin Kare-Karen Harajin Fito Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO 
  • Yadda Ake Tuwan Amala Da Miyar Uwaidu
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Har Yanzu Shugabanci NNPP Na Hannunmu – Tsagin Kwankwaso
  • Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
  • Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Sama Da 240 A Kebbi
  • Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 17: Tinubu Ya Kare Yadda Gwamnatinsa Ke Tafiyar Da Tsarin Rabon Arzikin Kasa