Aminiya:
2025-03-21@19:15:29 GMT

Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas

Published: 21st, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi caccaki Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas.

Kwankwaso ya ce matakin da Tinubu ya ɗauka ya saɓa doka kuma barazana ne ga dimokuraɗiyya.

Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe NAJERIYA A YAU: Illar Sare Itatuwa Ga Sauyin Yanayi Da Lafiyarmu

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Kwankwaso ya gargaɗi cewa irin wannan matakin na iya kafa mummunan misali da kuma illata dimokuraɗiyya a Najeriya.

Kwankwaso, ya ruwaito yadda rikicin siyasa da ya haifar da soke zaɓen 1993, inda ya jaddada cewa ‘yan majalisa su daina ɓata lokacinsu kan abubuwan da ba su dace ba.

“Majalisa tana da alhakin sa ido kan ayyukan ɓangaren zartarwa, ba wai kawai yarda da duk abin da ta ce ba.

“Abu ne mai matuƙar tayar da hankali ganin yadda Majalisar Tarayya ta 10 ta fi kowace zama ‘yar amshin shata ga ɓangaren zartarwa,” in ji shi.

Tsohon gwamnan ya kuma soki yadda Majalisar Tarayya ta gaggauta amincewa da matakin Shugaba Tinubu ba tare da bin ƙa’idojin da kundin tsarin mulki ya tanada ba.

“Kundin tsarin mulki ya fayyace yadda ake yanke hukunci kan irin wannan matsala, amma ‘yan majalisa sun zaɓi amfani da murya wajen zaɓe, wanda hakan yana janyo shakku kan sahihancin lamarin.

“Gaggawar amincewa da dokar ta-ɓaci da zata kifar da gwamnatin da aka zaɓa, cin fuska ne ga dimokuraɗiyya,” in ji shi.

Kwankwaso ya kuma yi gargaɗi kan shigar sojoji cikin harkokin mulki, inda ya bayyana cewa hakan tamkar komawa baya ne bayan ci gaban da aka samu tsawon shekaru 26 na dimokuraɗiyya.

Ya bayyana damuwarsa cewa wannan matakin na iya zama wata dabara ta murƙushe jihohin da ba sa tare da jam’iyya mai mulki.

“A matsayinsa na wanda ke da’awar kare dimokuraɗiyya, Shugaba Tinubu ya kamata ya fi kowa fahimta cewa kawo sojoji cikin mulki hatsari ne.

“Wannan matakin ba wai kawai barazana ne ga zaman lafiya ba, yana iya zama hanyar kama-karya idan ba a dakatar da shi ba,” in ji Kwankwaso.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Kwankwaso Kwankwaso ya

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar wakilai ta amince da dokar ta-ɓaci a Ribas

Majalisar Wakilai ta amince da ayyana dokar ta-ɓaci da Shugaba Bola Tinubu ya yi a Jihar Ribas.

Majalisar ta yanke wannan shawara ne a ranar Alhamis, ta hanyar kaɗa ƙuri’a da baki, inda ’yan majalisa 243 suka halarta.

Muhimman ayyuka 8 a goman ƙarshe na Ramadan Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a Abuja

A matsayin wani ɓangare na matakan dokar ta-ɓaci, majalisar ta bayar da shawarar kafa kwamiti domin dawo da zaman lafiya a jihar.

Hakazalika, majalisar za ta karɓi ragamar gudanar da ayyukan Majalisar Dokokin Jihar Ribas na tsawon watanni shida.

Me Ya Sa Aka Ayyana Dokar Ta-ɓaci?

Matakin ya biyo bayan rikicin siyasa da ya ƙi ya ƙi cinyewa a Jihar Ribas.

Shugaba Tinubu ya yanke wannan shawara ne sakamakon tashe-tashen hankula da rikicin shugabanci a jihar.

Gwamna Siminalayi Fubara na takun-saƙa da Majalisar Dokokin Jihar da wasu jiga-jigan ’yan siyasa musamman waɗanda ke tsagin tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike, lamarin da ya jefa jihar cikin tashin hankali.

Domim shawo kan matsalar, Tinubu ya naɗa Tsohon Babban Hafsan Rundunar Sojin Ruwa, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), a matsayin sabon mai kula da jihar.

Hakan ya sa Gwamna Fubara da wasu manyan jami’ai, ciki har da iyalansa, suka bar gidan gwamnatin jihar.

Ana ci gaba da sa ido kan halin da ake ciki a jihar, yayin da gwamnati ke ƙoƙarin tabbatar da doka da oda a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Yaba Wa Majalisar Dokoki Kan Amincewa Da Dokar Ta-Ɓaci A Jihar Ribas
  • Dokar Ta-Ɓaci: Tinubu Ya Kauce Hanya, Ya Ci Zarafin Dimokuraɗiyya A Ribas – Sambauna
  • Mun Yi Watsi Da Ayyana Dokar Ta-Ɓaci Da Tinubu Ya Yi A Ribas – Shugabannin Adawa
  • Majalisar wakilai ta amince da dokar ta-ɓaci a Ribas
  • Fubara ya magantu bayan ayyana dokar ta ɓaci a Ribas
  • Atiku Ya Soki Tinubu Kan Ayyana Dokar Ta-ɓaci a Jihar Ribas
  • Cire Gwamna Fubara ya saɓa wa Kundin Tsarin Mulki — Lauyoyi
  • Waiwaye: Jihohin Da Aka Taɓa Sanya Dokar Ta-ɓaci A Nijeriya
  • An shiga zaman ɗar-ɗar yayin da sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Ribas