HausaTv:
2025-04-13@05:49:21 GMT

Tunisiya : Kaïs Saïed, ya kori firaministansa Kamel Madouri

Published: 21st, March 2025 GMT

Shugaba Kaïs Saïed na Tunisiya ya kori firaministan kasar Kamel Madouri,  da aka nada a watan Agustan da ya gabata yayin wani gagarumin garanbawul a majalisar ministocin kasar a daren jiya Alhamis.

Wata sanarwa da fadar shugaban kasar ta fitar ta ce an maye gurbin firaministan kasar Madouri nan take inda aka maye gurbinsa da Sarra Zaafrani Zenzri, ministar kayan aiki.

Sanarwar ta ce sauren mambobin gwamnatin zasu ci gaba da aikinsu.

Garan bawul na shugaban kasar ta Tunisia a baya baya nan shi ne na ranar 6 ga watan Fabrairu inda ya sallami ministan kudinsa Sihem Boughdiri Nemsia da tsakar dare, tare da maye gurbinsa da alkalin kotun Michket Slama Khaldi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Macron :  Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa

Shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron, ya ce kasarsa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa nan da watanni masu zuwa.

Ya ce hakan na iya faruwa a farkon watan Yuni nan wannan shekarar a taron Majalisar Dinkin Duniya da za a gudanar a New York.

kawo yanzu, Kasashe 147 ne suka amince da yankin na Falasdinawa a matsayin kasa mai yanci.

Kasashen Sifaniya da Ireland da Norway su ne na baya-bayan nan da suka nuna amincewarsu a watan Mayun bara da yankin na Falasdinawa a matsayin kasa mai yanci, matakin da ya fusata Isra’ila.

Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa da dama dai na ganin samar da kasashe guda biyu Falasdinu da Isra’ila shi ne gimshikin samar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
  • Xi Jinping Zai Ziyarci Kasashen Vietnam Da Malaysia Da Cambodia
  • Xi Jinping Ya Gana Da Firaministan Spaniya
  • Shugaban Kasar Amurka Yace Yana Kokarin cimma yarjeniya da kasar China Dangane da Tiktok
  • Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka
  • Sudan ta kai karar Hadaddiyar Daular Larabawa a Kotun ICJ
  • Macron :  Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa
  • An Sace Dalibin Jami’ar Tarayya Birnin Kebbi