Babu ’yan adawan da za su iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027 — Ganduje
Published: 21st, March 2025 GMT
Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa babu wata gamayyar ’yan adawa da za ta iya hana Shugaba Bola Ahmed Tinubu lashe wa’adi na biyu a zaɓen 2027.
Ya yi wannan jawabi ne domin mayar da martani ga sabuwar haɗakar ’yan adawa da Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, da wasu shugabanni suka kafa.
A yayin taron manema labarai da Atiku ya gudanar a Abuja a ranar Alhamis, ya soki yadda Tinubu ke tafiyar da mulki, musamman batun ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas.
Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da Tsohon Gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha, da wasu ’yan siyasa sun hallara, inda suka bayyana shirin haɗa kai domin karɓe mulki daga hannun Tinubu a 2027.
Sai dai Ganduje ya yi watsi da wannan yunƙuri, inda ya bayyana cewa tafiyar ba za ta yi tasiri ba.
“Babu wata yarjejeniya ko haɗa kai da za ta hana ’yan Najeriya sake zaɓen Tinubu a 2027,” in ji shi a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan wayar da kan jama’a, Cif Oliver Okpala, ya fitar.
Ya ce irin nasarorin da Tinubu ya samu tun bayan hawansa mulki ne zai tabbatar da nasararsa.
“Tabbas Tinubu zai sake lashe zaɓe saboda irin ci gaban da ya kawo tun bayan da ya zama shugaban ƙasa,” in ji Ganduje.
Haka kuma, ya ce wannan sabuwar haɗakar ’yan adawa ba za ta yi tasiri ba, domin ’yan siyasar da ke ciki na da manufofi daban-daban.
“Ku manta da waɗannan tarukan na ‘yan siyasa da maganganunsu marasa tushe, domin yawancinsu ba su da wata makoma ta siyasa,” in ji shi.
“Haɗin gwiwarsu – kama daga kan jam’iyyar LP zuwa PDP da SDP – na ƙunshe da mutanen da ke da ra’ayoyi daban-daban da kuma son zuciya. Ba za su taɓa iya cimma muradi na siyasa ba.”
Wannan martani na Ganduje na nuni da cewa zaɓen 2027 zai kasance mai ɗaukar hankali tare da fafatawa mai zafi tsakanin ɓangarorin siyasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Adawa adawa Dokar Ta Ɓaci Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
Bam ya kashe mutum 4 da jikkata wasu a Borno
Aƙalla fasinjoji huɗu ne suka mutu yayin da wasu huɗu suka jikkata sakamakon fashewar wani bam a ƙarƙashin wata motar kasuwanci a ƙaramar hukumar Biu ta Jihar Borno.
Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta tabbatar ta afkuwar lamarin.
Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a BenuweMajiyoyin leƙen asiri sun shaidawa Zagazola Makama cewa, lamarin ya faru ne a ranar 19 ga Maris, 2025, da misalin ƙarfe 2:30 na rana a lokacin da wata mota ƙirar Golf 3 ta Wakil Fari ta tashi daga garin Kimba zuwa garin Biu.
Bayan sun isa mahaɗar Sabon Garin Kimba, motar ta taka wata nakiya (IED), wanda ya kai ga fashewa da ta kashe fasinjoji mata uku da fasinja namiji guda nan take.
Majiyar na cewar wasu fasinjoji hudu kuma sun sami raunuka daban-dabam kuma nan da nan an kai su babban asibitin Biu don yi musu jinya.
Daga bisani likitoci sun tabbatar da mutuwar wadancan mutane huɗu sannan aka ajiye su a ɗakin ajiyar gawa na asibitin kafin a miƙa su ga ’yan uwansu don yi musu jana’iza.
Bincike na farko ya nuna cewa ’yan ta’addar ISWAP ne suka dasa waɗannan bama-bamai (IEDs) a tunanin sojoji za su taka.
Jami’an soji sun tabbatar da faruwar hakan, tare da duba ƙarin barazanar da ake fuskanta daga wadannan ‘yan ta’addan don tabbatar da tsaro ga masu amfani da hanya.
Hukumomi sun kuma ƙaddamar da gangamin wayar da kan al’umma kan haɗarin bama-bamai da ba su fashe ba, don kaucewa faruwar lamari irin ya hakan.