Leadership News Hausa:
2025-04-14@07:36:30 GMT

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

Published: 21st, March 2025 GMT

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

Shi wannan azumi, na wani lokaci ya fi na wani lokaci kamar an so a dinga yin azumi sau Uku a cikin kowanne wata, lokacin kwanan wata yana 13 da 14 da 15, wannan kwanaki hasken wata ya fi haske a cikinsu, to kamar yadda suke haske haka zuciyarka za ta kara haske sabida saduwa da hasken, sannan kuma hawa-hawa na musulunci guda Uku ne (Islam da Iman da Ihsan) to wanda ya riski wannan kwanaki Uku kamar Ya hau dukka wannan Matakan addinin ne.

Akwai azumin Litinin da Alhamis, azumin ranar Litinin Annabi (SAW) ne yake yi, an tambaye shi cewa Ya Rasulullahi sabida me kake azumin ranar Litinin? sai ya ce ranar ce aka haife ni, ina godiya ga Allah. To duk wanda ya yi azumin ranar Litinin ya yi koyi da Annabi (SAW) ne. Azumin ranar Alhamis kuma, Annabi (SAW) ya ce ranar ake nade ayyukan bayi na mako zuwa ga Ubangijinsu Rabbul Izzati, ina kwadayin a kai aikina ga Ubangiji ina azumi. Akwai sauran azumomin nafila da yawa.

Akwai babban azumin nafila da ake cewa ‘Na Annabi Dawudu’: Annabi Dawudu Mutum ne sarki mai ibada, yana daga cikin Ibadarsa azumi. In ya yi azumi yau, gobe sai ya ci abinci, haka ya kasance yanayi a rayuwarsa, idan ya rayu shekaru 60 – shekaru 30 ya yi azumi.

Allah yana gode wa Dan’adam in ya ce zai yi azumi duk ranar da yake so sai dai ba a so ya ware wata rana kamar Jumu’a ko Asabar ya dinga azumtarsu duk sati. Lallai azumi yana da falala sosai.

Allah ya wajabta mana azumi kamar yadda ya wajabta ma wadanda suka zo kafin mu.
An karba hadisi daga Mu’azu bin Jabal yana cewa: “Manzon Allah (SAW) bayan ya yi Hijira zuwa Madina, sai wata rana, Yahudawan Madina duka suka tashi da Azumi – Ashura, sai Annabi (SAW) Ya tambayesu lafiya, sai suka ba shi amsa da cewa ai wanna ranar ce Allah ya tseratar da Annabi Musa ya hallakar da Fir’auna, sai Annabi (SAW) yabce mu muka fi cancanta da Musa”. Annabi (SAW) ya yi umarnin cewa kowa ya ci gaba da azumin, shekara mai zuwa Allah ya saukar da azumin watan Ramadana, Annabi (SAW) ya ce Allah ya ba mu namu wanda ya so ya ci gaba da na Ashura, har Annabi (SAW) ya koma ga Allah yana azumin Ashura, azumin yana daga cikin manyan azumin Nafila a addinin Musulunci.

Ya zo cewa Annabi (SAW) ba ya barin azumin kwana Uku na kowanne wata. Idan mutum yana yin azumin kwana Uku na kowanne wata za a rubuta masa ladan kwana 30, sabida kowanne aiki daya ana rubuta masa goma, don haka azumin kwana uku dai-dai yake da uku sau Goma, Talatin kenan.

Allah ya wajabta azumin Watan Ramadana ga al’ummar musulmi bakidaya, amma a farko masu hali (dukiya) ciyarwa suke, marasa dama kuma su yi azumi, har sai da Allah yace “Wa’anta sumu khairullakum” sannan ya zama wajibi a kan kowa. Amma har gobe, yana nan marasa lafiya su kididdige kwanukan da suka tsere musu su biya a wasu ranaku bayan watan Ramadana, wadanda ba za su iya azumtar watan ba su ciyar, matafiyi in ba zai iya azumi cikin tafiyar ba, shi ma ya ciyar.

Yana daga cikin falalar watan Ramadana, Annabi (SAW) ya ce idan Watan Ramadana ya zo, duk kofofin Aljannah bude su ake yi, duk kofofin wuta kuma sai a kulle, kuma sai a kulle duk shaidanu, sai ka ga masallatai duk sun cika, sabida abokin yawon shaidancin an kulle shi. Ba ana nufin Aljannu da suke kama mutane ba na rashin lafiya, wannan ciwo ne, lada za a bai wa majinyacin, abokin yawon shaidancin ake daurewa.

Nasa’i ya ruwaito cewa kullum mai kira zai yi kira a cikin dare, yana cewa “ya kai mai neman alheri taho, ga watan alheri ya zo, ya kai mai neman sharri kame, wannan ba watan sharri ba ne.”

Wasu daga cikin Malamai sun tafi cewa ‘Ramadana’ sunan Allah ne sabida Hadisin Abi Hurairah da yake cewa “kar ku ce Ramadana ya zo, sabida Ramadana suna ne daga cikin sunayen Allah”. Allah a Littafinsa cewa ya yi “Shahru Ramadana…” Amma ba laifi in an ce Ramadana ya zo sabida ana nufin watan Ramadana.

Allah ya saukar da mafificin littafi (Alkur’ani) a cikin watan Ramadana, a mafificin dare (Lailatul Kadri).

An karba daga Abdullahi bin Abbas, Allah ya yarda da su, yake cewa “Allah Ya saukar da Alkur’ani daga lauhil mahfuzi izuwa saman Duniya (a cikin Ramadana aka saukar da alkur’ani daga lauhil mahfuzi zuwa saman Duniya, a dakin Baitul ilimi), Mala’ika Jibril (AS) shi kuma daga nan yake debo ayoyinsa zuwa ga Annabi (SAW), sai da ya shafe shekaru 23 yana kan wannan aikin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: watan Ramadana azumin ranar

এছাড়াও পড়ুন:

Darasi daga rayuwar Dakta Idris AbdulAzeez Dutsen Tanshi

Rasuwar Sheikh Dakta Idris Abdulazeez Dutsen Tanshi rasuwa ce da ta jijjiga al’ummar Nijeriya da ma ƙasashen ƙetare, bisa la’akari da irin faɗakarwarsa da karantarwarsa da gwagwarmayarsa.

Hakan ya jawo dandazon al’ummar Musulmi suka halarci sallar jana’izarsa kuma fitattun mutane da malamai suka yi ta yin ta’aziyyar rasuwarsa.

Lokacin da Malamin yake raye kusan a kulum sai ya gabatar da huɗuba ko darasi na wayar da kan al’umma ko kuma ilmantar da su kan wani abu mai muhimmanci a masallacinsa da makarantarsa.

A ’yan shekarun nan Allah Ya jarrabe shi da rashin lafiya, wanda a sanadiyyar haka ya xauki tsawon lokaci ba a ji huɗubarsa ko karantarwarsa ba da suke xaukar hankalin dubban masu sauraro a faɗin Afirka, lamarin da ya jawo damuwa a tsakanin almajirai da kuma al’umman da ke bin karantarwarsa.

Rahotanni sun bayyana cewa, Malamin ya ɗauki lokaci mai tsawo yana fama da rashin lafiyar, kuma a wasu lokutan yana zuwa jinya, ya dawo, ya ci gaba da koyarwa kamar yadda ya saba.

Dakta Idris ya rasu ne daren Alhamis 4 ga watan Afrilun 2025, a gidansa da ke Bauchi bayan ya dawo daga jinya daga ƙasar Indiya.

Dakta Tauhid kamar yadda ake yi masa laƙabi, a bana ma bai samu gabatar da wa’azin da ya saba gabatarwa ba duk shekara cikin watan azumi kamar dai yadda bai yi ba a bara ba sakamakon rashin lafiya.

Malamin ya yi suna wajen karantar da Tauhidi da dogewa a kan gaskiya ko faɗar gaskiya komai ɗacinta ba tare da tsoron kowa ba ko kuwa shakka.

A lokacin da yake raye ya sha gwagwarmaya walau da malamai ko da ’yan siyasa waɗanda suke samun savanin fahimta da shi, musamman wajen ɗabbaƙa wata sunna ko kuma yi musu raddi kan wasu kurakurai da ya fahimta.

Dakta Idris mutum ne mai gudun duniya da ba ya shayin ɓoye fahimtarsa a kan duk wasu lamura da suka shafi addini ko siyasa ko da kuwa yin hakan zai zamo mai hatsari a gare shi.

Marigayin ya sha fama da tashe-tashen hankula da dama da kuma rashin jituwa da gwamnatocin baya a Jihar Bauchi, da ma samun savani da malaman ƙungiyoyin addinin Musulunci, wanda hakan ya sanya aka xaure shi a lokuta da dama tare da sanya shi yin gudun hijira ta wani ɗan lokaci.

Duk da irin saɓanin fahimta da yake yawan samu da malamai da kuma ’yan siyasa, da yawa daga cikinsu sun fito, sun yi addu’oi’n neman gafara gare shi, tare da bayyana shi a matsayin wani ginshiƙi na jaddada addini ta hanyar ƙarfafa tauhidi da ya shafe fiye da shekara 30 yana yi.

Hatta ma Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulƙadir Muhammed, wanda a zamanin mulkinsa saboda savanin da suka samu, an kai Dokta Idris gidan gyaran hali har sau biyu, ya je, ya yi ta’aziyyar rasuwar Malamin inda ya ce, ya yafe masa abin da duk ke tsakaninsu har ma ya yi alƙawarin mayar wa ɗaliban Malam Idris filin Sallar idi da a da gwamnatinsa ta ƙwace daga hannun marigayin.

Wasu daga cikin waɗanda suka yi mu’amala da malamin, sun bayyana shi da cewa, mutum ne mai godiyar alherin da aka yi masa kuma yana da zumunci da kyauta da yawan alheri.

Musa Azare ya ce, ‘‘ko kafin rasuwarsa na kira wani makusancin Imam Idris don in ba shi saƙo ya isar masa na gaisuwa da addu’ar Allah Ya ba shi lafiya, kamar yadda daman ta hanyar wannan mutumin muke sada zumunci da Malam. Sai mutumin ya ce min jikin malam fa ya yi tsanani. A taya shi da addu’a.”

Bayanai sun nuna, a asibitin da Malam ya je a ƙasar Indiya, sun nemi ya zauna a wajensu domin yana shan wasu magunguna, kuma magungunan za a xauki tsawon lokaci ana shan su, kafin a yi masa tiyata da kuma kula da shi a-kai-akai. Amma sai ya ce, shi ba zai zauna, ya mutu cikin waɗanda ba Musulmai ba. Gara ya dawo gida Nijeriya, idan ya gama shan magungunan sai ya koma asibiti. Idan kuma lokacinsa ne ya yi, to mutuwa ta riske shi cikin iyalai da ’yan uwansa Musulmi.

Dakta Tauhid ya gina makarantun sakandare da Kwalejin Horar da Malamai Ilimi Mai Zurfi wato, ‘College Of Education Dutsin Tanshi Bauchi’, kuma yana ba da ilimi kyauta ga ’ya’yan talakawa da marayu waɗanda ba su da halin biyan kuɗin karatu.

Har ma wani lokaci a watan Oktoba na shekarar 2023, saboda tsananin ƙuncin talauci da jama’a suka shiga, Malam Idris Abdul’aziz Bauchi Hafizahullah ya yafe wa duk wani ɗalibi kuɗin rajistar zangon karatu na farko a matakin NCE da Diploma a makarantarsa ta College of Education Dutsen Tanshi.

Ba Musulmi ne kawai suka ji daɗin mu’amala da malamin ba, har ma da Kiristoci, inda hatta Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai ta Tarayya, Honarabul Yakubu Dogara a saƙon ta’aziyyarsa ya ce, ‘‘na sami labari mara daxi na rasuwar ɗan uwana, abokina kuma ɗan kishin ƙasa, Sheik Dakta Idris Abdulazeez. Na san malam da alaƙa ta ƙut-da-ƙut da kuma dangantakarmu ta ƙara ƙarfi kuma mun haɗa kai a matsayinmu na ’yan uwa, musamman a shekarar 2023 yayin da muke haɗa kan ’yan Bauchi don ƙwato kansu daga sarƙaƙiyar da ta ɗaure su.

“Zan iya cewa zuciyar malam ta kasance tana jin tausayin waɗanda aka zalunta. Ya kasance mai jaruntaka, ba shi da tsoro kuma a kodayaushe ba ya jin tsoron faɗin gaskiya ga mai mulki ko da wane ne yake kan mulkin. Shi ba malamin addinin Musulunci ba ne kawai, shugaba ne marar son kai kuma mai taimakon jama’a da ba a saba gani ba. Kowa zai yi kewar sa sosai,”

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya turo Babban Mai Ba shi Shawara kan Harkokin Tsaro, Malam Nuhu Ribadu, inda ya zo tare da Sanata Shehu Buba wanda ya biya duk bashin da ake bin malamin. Haka ma Shugaban Gwamnonin Arewa, Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya isar da ta’aziyyar dukkan gwamnonin game da rasuwarsa.

Gwamna Inuwa ya ce, rasuwar Sheik babban rashi ne, ba wai ga iyalansa da al’ummar Jihar Bauchi kaɗai ba, har ma da fannin ilimin addinin Musulunci, musamman ga waɗanda suka samu ƙwarin gwiwa suka samu ilimi mai nagarta daga hikima da jagoranci irin na malamin.

Ya miƙa sakon ta’aziyyar gwamnonin ga iyalan mamacin da gwamnatin Jihar Bauchi da sauran al’ummar Musulmi. Ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya saka wa Dakta Idris da Aljannar Firdausi.

A cikin wasiyyarsa, Marigayi Malma Idris ya hana ɗaukar hoto a wajen jana’izarsa kuma ya soke taron ta’aziyya ko na tunawa da shi a gidansa. Haka kuma ya hana mutane yin turereniya wajen ɗaukar gawarsa da kuma shiga maƙabartar da takalmi. Dubban mutane ne suka yi dandazo kuma suka halarci jana’izarsa

Imam Idris ya yi shekara 58 a duniya kafin rasuwarsa, inda ya yi karatun addini a nan gida Nijeriya da ƙasar Saudiyya, inda ya samu digiri a fannin shari’ar Musulunci a Jami’ar Musulunci ta Madina, ya kuma yi digiri na biyu a Jami’ar Jos da kuma digiri na uku a fannin shari’a a wata jami’ar da ke qasar Sudan.

Za a ci gaba da tuna Malam da irin darussan da ya koyar, musamman yadda ya shahara da wa’azin da ba tsoro, wanda galibi yana sukar manufofin gwamnati, musamman kan batutuwan da suka shafi mulki da cin-hanci da rashawa da take haƙƙin al’umma. Marigayin ya rasu ya bar mata da ’ya’ya da dama da kuma tarin ɗalibansa da dubban masoya a faɗin duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO 
  • Tsohon Kocin Super Eagles, Christian Chukwu, Ya Rasu Yana Da Shekaru 74
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 108
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
  • Darasi daga rayuwar Dakta Idris AbdulAzeez Dutsen Tanshi
  • Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
  • Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Sama Da 240 A Kebbi