Aminiya:
2025-03-21@19:22:22 GMT

Gwamnatin Yobe na ciyar da almajirai a Tsangayu 85 kullum

Published: 21st, March 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Yobe ta kafa cibiyoyin bayar da abinci 85 domin samar wa almajirai abinci a dukkanin Ƙananan Hukumomin 17 na jihar, a lokacin azumin Ramadan.

Sakataren zartarwa na Hukumar Ilimin Larabci da Addinin Musulunci ta Jihar Yobe, Malam Umar Abubakar ne, ya bayyana hakan a wata hira da Daily Trust a ranar Alhamis.

Sanƙarau ta kashe mutum 55 saboda rashin tsafta a Kebbi Dabarun Rabauta Da Kwanaki 10 Na Ƙarshen Ramadan

“Muna bai wa makarantun Tsangaya 85 kayan abinci 85, biyar a kowace Ƙaramar Hukuma, inda muke ciyar da almajirai tsakanin 300 zuwa 400 a kowace makaranta,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa Gwamna Mai Mala Buni ne, ya amince da wannan shiri domin tallafa wa yara marasa galihu a jihar.

Baya ga haka, gwamnatin ta buɗe manyan cibiyoyin ciyarwa guda uku a Damaturu domin ciyar da sama da almajirai 2,000 da wasu mabuƙata.

Abubakar, ya bayyana cewa hukumar na kuma samar wa almajiran kayan sakawa.

“Mu na da alhakin tabbatar da cewa waɗannan yara sun ji cewa suna cikin al’umma.

“Zuwa yanzu mun ɗinkawa sama da 850 daga cikinsu tufafi, kuma Insha’Allah, muna da shirin ƙara wannan adadi a nan gaba,” in ji shi.

Ya gode wa gwamnan saboda goyon bayansa tare da kira ga sauran gwamnatoci da masu hali da su taimaka wajen tallafa wa yara marasa ƙarfi a cikin jama’a.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Almajirai ciyarwa gwamnati Tsangaya

এছাড়াও পড়ুন:

Jakadan Amurka Ya Ziyarci Sarkin Zazzau Domin Karfafa Alakar Amurka Da Najeriya

Jakadan Amurka a Najeriya, Richard Mills Jr, ya ziyarci mai martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmad Bamalli domin ingantawa da karfafa hadin kan al’adu.

 

Jekadan ya ce Amurka ta jajirce sosai kan alakar da Najeriya ya kara da cewa; ‘ muna so mu zurfafa shi kuma mu ƙarfafa shi.”

 

A cewarsa, hanyar da ta fi dacewa wajen zurfafa wannan alaka ita ce ta haduwa irin wannan da za mu ji ta bakin juna.

 

“Ina sa ran jin ta bakinku kan abubuwan da kuke yi na karfafa hadin kan addini a tsakanin al’umma, damar ilimi da kuma damar yin aiki ga jama’ar ku.

 

“Abin da Amurka za ta iya yi don haɓaka ƙarin alaƙa da kuma matakan da za mu iya ɗauka don zurfafa dangantakarmu,” in ji Mills.

 

Da yake mayar da jawabi, Mai martaba Sarkin Zazzau ya yabawa ma’aikatar harkokin wajen Amurka kan bude cibiyar kula da harkokin a Amurka a jami’ar Ahmadu Bello.

 

Bamalli ya yi fatan wannan cibiar da aka kira da Window on America da turanci ta zama matakin samar da ingantacciyar dama tsakanin Amurka da masarautar Zazzau da jihar Kaduna.

 

Ya kara da cewa masarautar na da alaka mai tsawo da ofishin jakadancin Amurka inda ya kara da cewa tawagogin ofishin jakadanci sun kasance suna halartar Dabar karshen watan Ramadan a Zariya.

 

“Amma hakan ya tsaya cik tsawon wasu shekaru saboda rashin tsaro, amma za mu iya cewa zaman lafiya ya dawo ga al’ummarmu.

 

“Saboda haka, muna fatan mambobin ofishin jakadancin da sauran jami’an diflomasiyya za su ci gaba da halartar bukukuwan Sallah Durbar,” in ji Bamalli.

 

COV/ Ibrahim Suleiman

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uwargidan Gwamnan Jihar Kaduna Ta Raba Abinci, Tufafi Ga Marayu, Mabukata Da Malamai
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Taimakon NAMA Don Gudanar Da Aikin Hajjin Bana Cikin Nasara 
  • Sojojin Yamen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Tashar Jiragen Sama Na Bengerion A HKI
  • Jakadan Amurka Ya Ziyarci Sarkin Zazzau Domin Karfafa Alakar Amurka Da Najeriya
  • Gobara ta kashe yara 3, ta jikkata 13 a Yobe
  • Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin Ribas 
  • Za Mu Bi Doka Domin Dawo Da Haƙƙinmu – Fubara
  • Fubara ya magantu bayan ayyana dokar ta ɓaci a Ribas
  • An shiga zaman ɗar-ɗar yayin da sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Ribas