An Bukaci Shugaban Kasa Ya Sa Ido Ga Aikin Biyan Kudaden Fansho
Published: 21st, March 2025 GMT
An bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya tabbatar da sa ido sosai kan yadda aka fitar da kudade naira biliyan 758 domin warware duk wasu basussukan fensho da ake bin su domin hana yin zagon kasa.
A cikin wata sanarwa da kungiyar Muslim Media Watch Group ta fitar, kodineta na kasa, Alhaji Ibrahim Abdullahi ya kuma yabawa shugaba Tinubu kan matakin da ya dauka na ragewa ‘yan fansho na tarayya daga halin kuncin da suke ciki.
A cewar sanarwar, dole ne a sanya ido sosai kan sabuwar manufar domin hana duk wani zagon kasa daga wasu Ma’aikatan Asusun Fansho (PFA) da ake zargi da batawa wasu ‘yan fansho da suka yi rajista da su rai.
Ya bayyana cewa wasu Ma’aikatan Asusun Fansho sun kara wa ‘yan fansho matsalolin da suke fuskanta ta hanyar jinkirta biyan su fansho kusan shekaru 2 bayan sun yi ritaya.
Ta ce duk irin wadannan laifuffuka da rashin iya aiki sun karfafa cin hanci da rashawa a sassan al’umma na tattalin arzikin kasa.
Sanarwar ta yi kira da a samar da cikakken tsari da ingantaccen tsarin sa ido daga fadar shugaban kasa da hukumar fansho ta kasa PENCOM wajen magance matsalolin ‘yan fansho gaba daya.
Tana kira ga Gwamnonin Jihohi a fadin Tarayya da su yi koyi da Gwamnatin Tarayya wajen biyan basussukan da ake bin Jihohi da Kananan Hukumomi.
Sanarwar ta kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta yin la’akari da yin kwaskwarima ga dokokin gudanar da shari’ar laifuka (ACJ) domin hukunta laifukan tattalin arziki da ake tafkawa a Najeriya.
REL/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce shirye-shirye sun yi nisa game da aikin Hajjin shekarar 2025 a jihar.
Daraktan Hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ne ya bayyana hakan ga Radio Nigeria a hedikwatar hukumar da ke Dutse.
A cewarsa, zuwa yanzu hukumar ta mika sunayen maniyyata fiye da dubu ɗaya da suka kammala biyan kuɗin aikin Hajji daga jihar zuwa ga Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON).
Ya ce tuni aka fara shigar da waɗanda suka kammala biyan kuɗin cikin tsarin neman biza.
Labbo ya bayyana cewa hukumar ta biya Hukumar Hajji ta Ƙasa kuɗi naira biliyan takwas a madadin alhazan jihar na shekarar 2025.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce ana gudanar da tarukan bita ga maniyyata a kullum, a kananan hukumomi 27 na jihar, ta hannun wasu malamai don ilmantar da su game da aikin hajjin.
Ya ƙara da cewa hukumar za ta raba jakunkuna da za su daukin nauyin kilo 8 da unifom ga jami’an yankuna da cibiyoyi domin rabawa mahajjatan.
Shugaban hukumar ya ja hankalin maniyyatan da su riƙa halartar traon bita saboda muhimmancinsa.
Ya yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da haɗin kai da yake ba hukumar domin samun nasarar gudanar da aikin hajji ba tare da wata tangarda ba.
Radio Nigeria ta ruwaito cewa Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta ware kujeru sama da 1,800 ga jihar domin aikin hajjin bana.
Usman Muhammad Zaria