Jiragen yakin HKI sun kai hare-hare a gabaci da kuma kudancin kasar Lebanon wanda yak eta yarjeniyar zaman lafiyan da HKI ta cimma da kungiyar Hizbullah mai lamba 1701 ta shekara ta 2006.

Tashar talabijin ta Presstv anan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran gwamnatin kasar Lebanon na cewa, jiragen yakin HKI sun kai hare-hare kan bayan kauyen taraya a gundumar ba’alabak, cikin lardin Ba’alabak Hermel, da kuma kan garin Shaara kusa da garin Jenta a dai dai kasar tsaunuka da ke yankin.

A kudancin kasar Lebanon kuma jiragen yakin HKI sun jefa makamai masu linzami har guda 4 a kan yakunan Jibaa da Snaya

Kafafen yada labaran HKI sun tabbatar da wannan labarin sun kuma nakalto sojojin kasar suna cewa sun kai hare-haren ne kan damdamalin cilla makamai masu linzami na kungiyar Hizbullah.

Sanarwan sojojin yahudawan ya ce: Sojojin HKI sun kai hari kan wuraren kungiyar Hizbullah, wadanda suke karkashin kasa a lardin Biqaa a kasar Lebanon.

Gwamnatin HKI a dole ta amince da tsagaita budewa juna wuta da kungiyar Hizbullah a ranar 27 ga watan Nuwamban shekarar da ta gabata, bayan asarorin na rayukan sojoji da tankunan yaki da kuma gine-gine masu muhimmanci wadanda kungiyar Hizbullah ta lalata a cikin yakin watanni 14 da suka fafata. Ta amince da kuduri kwamitin tsaro mai lamba 1701 na kwamitin tsaro ba tare da ta cimma ko guda daga cikin manufofin fara yakin ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kungiyar Hizbullah sun kai hare hare kasar Lebanon yakin HKI sun

এছাড়াও পড়ুন:

Tawagogin gwamnatin Kongo da kungiyar M23 sun isa  Doha domin tattaunawa

Jami’an Kongo da masu shiga tsakani na M23 sun isa Qatar domin tattaunawa don cimma yarjejeniyar tsagaita wuta.

Jami’an Kongo da masu shiga tsakani na kungiyar M23 sun isa Doha babban birnin kasar Qatar domin tattaunawa da nufin cimma tsagaita bude wuta da kuma kawo karshen fadan da aka shafe watanni ana gwabzawa a yankin, kamar yadda wasu majiyoyi hudu suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters a jiya Alhamis.

Wakilan tawagogin biyu sun tabbatar da kasancewarsu a babban birnin kasar Qatar, kuma sun ce za a yi ganawar ido-da-ido a ranar Laraba, amma har yanzu suna tattaunawa kan tsarin tattaunawar.

Dukkanin majiyoyi – jami’an gwamnati biyu da wakilan ‘yan tawaye – sun bukaci a sakaya sunansu saboda masu shiga tsakani na Qatar sun nemi kada su yi magana da manema labarai.

Qatar ta yi wata ganawa a watan da ya gabata tsakanin shugaban kasar Congo Felix Tshisekedi da takwaransa na Rwanda Paul Kagame. Wannan ita ce ganawa ta farko da shugabannin biyu suka yi tun bayan da kungiyar ta kaddamar da hari a ranar 23 ga watan Maris din da ya gabata. Yunkurin yin shawarwarin zaman lafiya na baya-bayan nan shi ne yunkurin kawo karshen rikicin da aka kwashe shekaru ana yi, wanda ya samo asali daga kisan kiyashin da aka yi a kasar Rwanda a shekara ta 1994.

Wata majiya da ke da masaniya kan shiga tsakani na Qatar ta shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters cewa bangarorin biyu sun yi wata ganawar sirri a birnin Doha a farkon wannan wata domin shirya tattaunawar sulhu. Sai dai har yanzu tattaunawar da aka shirya fara a ranar Laraba na fuskantar cikas.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara
  • Yemen Ta Maida Martani Kan Wasu Cibiyoyin Ajiyar Makamai A Yaffa Don Tallafawa Gaza
  • Tawagogin gwamnatin Kongo da kungiyar M23 sun isa  Doha domin tattaunawa
  • Hizbullah ta kirayi gwamnatin Lebanon da ta dauki mataki kan hare-haren Isra’ila
  •  Amurka Ta Kai Hare-hare A Yankunan Kasa Yemen
  • An Kafa Dokar Kai Da Komowa A Kudancin Kasar Syria
  • Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba
  • Sojojin Sama Na HKI Kimani 1000 Guda New Suka Bukaci A Kawo Karshen Yaki A Gaza
  • Ministan harkokin wajen Iran ya tattauna da takwaransa na Masar kan halin da ake ciki a yankin
  • Tarkon Mutuwa a Katsina: Hanyar Funtua zuwa Ƙanƙara