Shugaban tarayyar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bada umurnin a gudanar da bincike don gano abinda ya hadda hatsarin day a faru a kan gadar Karuk an titin Abuja Keffi a daren Labaran da ta gabata, wanda yayi sanadiyyar mutuwar mutane da kuma jikatan wasu.

Jaridar Premium Times ta nakalto shugaban kasar yana fadar haka tabakin mai bashi shawara kan al-amuran watsa labarai Bayo Onanuga a jiya Alhamis.

Shugaban ya bayyana alhininsa ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma fatan murmurewar wadanda suka ji rauni. Ya kuma bukaci a gaggauta gudanar da bincike don sanin abinda ya haddasa hatsarin day a kai da wannan asarar, don daukar matakan hana aukuwar irinsa nan gaba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum Shida Sun Mutu A Hatsarin Jirgi Mai Saukar Ungulu A Amurka

Wani jirgi mai saukar ungulu ya faɗa cikin kogin Hudson da ke birnin New York a Amurka.

 

Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun bayyana cewa mutum shida da ke cikin jirgin – fasinja biyar da direban jirgi guda sun mutu.

 

Magajin garin New York Eric Adams ya ce jirgin na ɗauke da wani iyali su biyar daga Spain har da yara uku.

 

Ya ƙara da cewa tuni aka tsamo gawarwakin mutum biyar ɗin daga ruwa.

 

Wakilin BBC ya ce har yanzu ana aikin ceto domin koƙarin zaƙulo tarkacen jirgin da masu bincike za su buƙata don gano abin da ya haddasa haɗarin.

 

Shaidu sun ce jirgin ya tarwatse ne tun a sama inda kuma ya faɗa cikin kogin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi
  • An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi 
  • An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
  • Mutum Shida Sun Mutu A Hatsarin Jirgi Mai Saukar Ungulu A Amurka
  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Ba Matan Arewa Ta Gabas Su Dubu Tallafin Naira Miliyan 50
  • Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 17: Tinubu Ya Kare Yadda Gwamnatinsa Ke Tafiyar Da Tsarin Rabon Arzikin Kasa
  • Gwamnati ta gargaɗi jihohi 30 kan ambaliyar ruwa
  • An kama masu garkuwa da mutane biyu a Yobe
  • E.U.  ta dauki wasu sabbin matakan kalubalantar harajin fito na Amurka
  • Rundunar Sojan Nijeriya Ta Fara Gasar Wasanni A Sakkwato