Kotun ƙoli ta tabbatar da Anyanwu a matsayin sakataren PDP
Published: 21st, March 2025 GMT
Kotun Ƙoli ta yanke hukunci tare da tabbatar da Samuel Anyanwu a matsayin halastaccen Sakataren Jam’iyyar PDP na Ƙasa.
Anyanwu, wanda na hannun daman Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike ne, ya shafe lokaci yana takun-saƙa da Sunday Ude-Okoye kan wannan matsayi.
Tinubu ya ba ni riƙon Ribas don wanzar da zaman lafiya — Ibas Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a RibasUde-Okoye ya samu goyon bayan wasu ɓangarori na jam’iyyar PDP bayan Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Enugu ta tabbatar da naɗinsa, biyo bayan hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ta tsige Anyanwu.
Sai dai, a ranar Juma’a, wani kwamitin alƙalan Kotun Ƙoli guda biyar, ya yanke hukunci cewa rikice-rikicen shugabanci a cikin jam’iyya al’amari ne na cikin gida, kuma ba hurumin kotu ba ne sai dai idan akwai wasu dalilai na musamman.
Mai shari’a Jamilu Tukur, wanda ya jagoranci hukuncin, ya bayyana cewa irin wannan shari’a za ta iya shiga hurumin kotu ne kawai idan ta ƙunshi karya doka, aikata laifi, ko saɓa wa yarjejeniya.
Rigima game da muƙamin sakataren jam’iyyar PDP na ƙasa, ta samo asali ne bayan Anyanwu ya ajiye muƙamin don yin takarar gwamna a Jihar Imo, amma bai samu nasara ba.
Yunƙurinsa na sake dawowa kan muƙamin ya jefa jam’iyyar cikin ruɗani.
Bayan Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da tsige shi a watan Disamban 2024, Anyanwu ya shigar da ƙara a Kotun Ƙoli, wacce a yanzu ta yanke hukunci, tare dawo da shi a matsayin halastaccen sakataren jam’iyyar PDP na ƙasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Anyanwu Sakatare Siyasa jam iyyar PDP tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta yanke wa tsohon Shugaban Peru ɗaurin shekaru 15
An yanke wa tsohon shugabar ƙasar Peru, Ollanta Humala hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari.
Wata kotu a ƙasar ce ta yanke masa hukuncin bisa samunsa da laifin halatta kuɗin haram a badaƙalar cin hanci da katafaren kamfanin gine-gine na Brazil Odebrecht ke yi don samun kwangila.
Dalilin da Kwankwaso zai dawo APC — Ganduje Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu ranar Juma’a da LitininHaka kuma, ita ma mai ɗakinsa, Nadine Heredia, an yanke mata makamancin wannan hukuncin, duk da cewa ba ta halarci zaman kotun ba, saboda haka alƙalin ya bayar da umarnin kamo ta.
Ollanta Humala, mai shekaru 62, ya kasance tsohon shugaban ƙasar Peru na biyu da aka samu da laifi, lamarin da ya sa nan take aka kai shi wani gidan yari da ke gabashin Lima, inda ake tsare da tsoffin shugabannin kasar Peru Alejandro Toledo da Pedro Castillo.
Wannan hukuncin na zuwa ne sama da shekaru uku da fara shari’ar Humala wanda ya mulki ƙasar Peru daga 2011 zuwa 2016 —amma dai lauyoyinsa sun bayanna cewa za su ɗaukaka ƙara.
Ma’aikatar Shari’a ta Amurka ta ce Kamfanin Odebrecht ya ba da cin hanci dala miliyan 788 a cikin shekaru goma ga gwamnatocin yankin Latin Amurka domin samun kwangilar gine-gine.
Kamfanin ya bayyana cewar ya bayar da dala miliyan 29 na cin hanci ga Peru a tsakanin 2005 da 2014.