Gwamnoni Na Kamun Kafa A Wurin Tinubu Don Hana Bai Wa Kananan Hukumomi ‘Yanci
Published: 21st, March 2025 GMT
“Amma gwamnoin sun ce a’a. Ba sa son hakan. Sun ce idan kudaden n ya kai ga CBN, ya nuna cewa gwamnatin tarayya ce take kulawa da komi.”
Majiyar ta ce tattaunawar Tinubu da gwamnoni ya bayyana cewa, gwamnonin na bukatar a kai kudaden zuwa bankunan kasuwanci nan take.
“Daya daga cikin gwamnonin ya ce idan har CBN ke kula da asusun, za su bukaci amincewa daga wurin akanta janar na Nijeriya.
Game da sakamakon ganawar, majiyar ta ce, “Sun ce ganawar ta haifar da da mai ido. Amma ban san abin da suka tsaya a kai ba. Suna aiki tare da wasu ma’aikata don su sami hanyar samun fita. Amma abu mafi muhimmanci shi ne, an rike kudaden kananan hukumomi. Ba a biya ba. Saboda wannan dambarwa.”
A tarihi, an dade ana jayayya kan kudaden kananan hukumomi, musamman domin ikon da ke tsakanin jihohi da kananan hukumomi.
A ranar 11 ga Yuli, 2024, kotun koli ta zartar da hukunci mai muhimmanci da ya tabbatar da bai wa dukkan kananan hukumomin kasar nan cin gashin kai.
Ya hukuncin ya bayyana cewa dole ne a biya kudaden kananan hukumomi kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.
Wannan ya biyo bayan karar da gwamnatin tarayya ta shigar, wadda ta nemi ta daukaka ‘yancin kananan hukumomi kamar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 ya tanada.
Kotun kolin ta jaddada cewa ba ya saba wa tsarin kundin mulki gwamnonin jihohi su ci gaba da kula da kudaden kananan hukumomi, inda ta bukaci a dunga tura wa kananan hukumomin kudadensu kai tsayi daga asusun gwamnatin tarayya.
Haka kuma hukuncin ya hada da tsarin samar da shugabannin kananan hukumomi ta hanyar dimokuradiyya ne kawai za su iya samun kudadensu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.
An samar da wannan tsarin ne don magance yadda gwamnonin jihohi suke nada kwamitocin rikon kwarya ko kuma masu kula da ayyukan kananan hukumomi ba tare da yin zabe ba.
A yanzu haka dai, CBN ya bukaci dukkan kananan hukumomi su mika bayanan asusunsu na tsawan shekaru biyu kafin a fara biyansu.
CBN Ya kuma soma bude asusun banki na kananan hukumomi wanda zai dunga tura musu kudadensu kai tsaye.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: gwamnatin tarayya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Yobe na ciyar da almajirai a Tsangayu 85 kullum
Gwamnatin Jihar Yobe ta kafa cibiyoyin bayar da abinci 85 domin samar wa almajirai abinci a dukkanin Ƙananan Hukumomin 17 na jihar, a lokacin azumin Ramadan.
Sakataren zartarwa na Hukumar Ilimin Larabci da Addinin Musulunci ta Jihar Yobe, Malam Umar Abubakar ne, ya bayyana hakan a wata hira da Daily Trust a ranar Alhamis.
Sanƙarau ta kashe mutum 55 saboda rashin tsafta a Kebbi Dabarun Rabauta Da Kwanaki 10 Na Ƙarshen Ramadan“Muna bai wa makarantun Tsangaya 85 kayan abinci 85, biyar a kowace Ƙaramar Hukuma, inda muke ciyar da almajirai tsakanin 300 zuwa 400 a kowace makaranta,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa Gwamna Mai Mala Buni ne, ya amince da wannan shiri domin tallafa wa yara marasa galihu a jihar.
Baya ga haka, gwamnatin ta buɗe manyan cibiyoyin ciyarwa guda uku a Damaturu domin ciyar da sama da almajirai 2,000 da wasu mabuƙata.
Abubakar, ya bayyana cewa hukumar na kuma samar wa almajiran kayan sakawa.
“Mu na da alhakin tabbatar da cewa waɗannan yara sun ji cewa suna cikin al’umma.
“Zuwa yanzu mun ɗinkawa sama da 850 daga cikinsu tufafi, kuma Insha’Allah, muna da shirin ƙara wannan adadi a nan gaba,” in ji shi.
Ya gode wa gwamnan saboda goyon bayansa tare da kira ga sauran gwamnatoci da masu hali da su taimaka wajen tallafa wa yara marasa ƙarfi a cikin jama’a.