Nasiru Ahali Shahararren masanin masana’antu a Kano ya rasu
Published: 21st, March 2025 GMT
Allah Ya yi wa Alhaji Nasiru Ahali, Shugaban Kamfanin Mainasara & Sons, rasuwa.
Marigayin wanda yake shahararren masanin masana’antu ne ya rasu yana da shekara 108.
Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina Kotun ƙoli ta tabbatar da Anyanwu a matsayin sakataren PDPA cewar majiyoyin na kusa da iyalan marigayin ɗan kasuwar ya rasu ne a wani asibiti da ke Kano a daren ranar Alhamis.
Ana girmama Ahali a matsayin ɗaya daga cikin jiga-jigan masanin asalin masana’antu a Kano. Ya yi ƙoƙari ya kafa tsarin kasuwanci na yau da kullun.
A tattaunawarsa da Daily Trust a shekarar 2018, marigayi Ahli ya bayyana cewa sana’arsa ta haɗa da buga littattafai, bugu takardu, masana’antar bulo, sana’ar fasa dutse, shigo da kaya, kwangilar gama-gari, bunƙasa kadarorin rukunin gidaje, ayyukan ƙarafa da sauransu.
A saƙon ta’aziyyar da ya aike wa iyalan marigayin ta hannun Babban Daraktan Yaɗa Labarai na Gidan Gwamnatin Kano, Malam Sanusi Bature Dawakin Tofa, Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf, ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ba ga iyalansa kaɗai ba, har da jiha da ƙasa da sauran al’ummar Musulmi baki ɗaya.
Ya bayyana marigayin a matsayin ɗaya daga cikin waɗanda suka kafa masana’antu, inda ya ce shi ne ya tsara tattalin arzikin jihar tare da taka muhimmiyar rawa a tsakanin ƙananan masana’antu da manyan masana’antu a jihar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: Jagora ya yi kira da a karfafa dogaro da kai a cikin gida domin dakile tasirin takunkumai
Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya taya al’ummar Iran murnar zagayowar lokacin bukukuwan Nowruz na sabuwar shekarar hijira shamsiyya da ake amfani da itya a hukumance a kasar Iran.
Ayatullah Khamenei ya bayyana hakan ne a wani sako da ya aikewa al’ummar kasar ta gidan telebijin na murnar shiga sabuwar shekara ta Farisa a yammacin wannan Alhamis.
Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya jaddada bukatar gwamnati da al’ummar kasar su ci gaba da zuba jari don karfafa azamarsu wajen tunkarar takunkumai na zalunci da masu girman kai na duniya suka kakaba ma kasar.
Ayatullah Khamenei ya jaddada cewa samar da kayayyaki na samun bunkasuwa ne idan aka ba da tallafin jari mai karfi.
Jagoran ya kuma yi Allah wadai da sabbin hare-haren da Isra’ila da take kaiwa Gaza, inda ya yi kira ga kasashen duniya baki daya da su nuna adawa da laifukan da Amurka da Isra’ila ke aikatawa a Gaza.
A yayin da ya koma kan batun kasar Yemen, Ayatullah Khamenei ya bayyana hare-haren da Amurka ke kai wa al’ummar kasar Yemen a matsayin wani laifi da ya zama wajibi a dakatar da shi.
Ya bayyana fatan alheri, nasara, da alheri ga al’ummar musulmi a cikin sabuwar shekara.