’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe
Published: 21st, March 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da wani jami’in Hukumar kiyaye haɗɗura ta ƙasa (FRSC) Nathaniel Terwanger Kumashe a ƙauyensa da ke ƙaramar hukumar Tarka a Jihar Benuwe.
An samu rahoton cewa wanda aka yi garkuwan ya taso ne daga Makurdi sansaninsa, domin halartar jana’izar ɗan uwansa da ya rasu a lokacin da aka ɗauke shi zuwa wani wuri da ba a san inda yake ba.
Wani kawun wanda aka yi garkuwan, tsohon mai baiwa gwamnan Jihar Benuwe shawara kan harkokin sufuri, Cif Yimam Aboh, ya shaidawa manema labarai a Makurdi ta wayar tarho cewa an ɗauke jami’in, Insfekta Kumashe a daren Laraba da misalin ƙarfe 10 na dare.
Ya ce, ’yan bindigar sun yi ta harbi don tsoratar da ’yan uwa da maƙwabta kafin su yi awon gaba da wanda suka yi garkuwan daga gidansu da ke Tse Aboh, Uchi-Mbakor a ƙaramar hukumar Tarka.
Ya kuma bayyana cewa, Kumashe ya koma gidansa ne bayan rasuwar ɗan uwansa wanda za a yi jana’izarsa a yau lokacin da masu garkuwar suka farwa gidan.
A halin da ake ciki, jami’ar hulɗa da jama’a ta Hukumar FRSC a Benuwe, Ngozi Ahula, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ƙara da cewa an kai rahoton lamarin ga ’yan sanda.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane jihar Benue
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace shugaban kasuwar kayan miya ta Akinyele a Oyo
Wasu ’yan bindiga sun kai hari Kasuwar Kayan Miya ta Akinyele, kusa da Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo, inda suka sace Shugaban Kasuwar, Alhaji Usman Yako.
Bayanan da muka samu daga shugabannin kasuwar sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7 na dare, jim kadan bayan an idar da sallar Magriba.
Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa Goman Ƙarshe: Dama ta ƙarshe ga mai neman rahamar AllahMataimakin Shugaban Kasuwar, Alhaji Abdul’aziz Abdulwasi’u (Dan Kashi), ya tabbatar da faruwar lamarin.
“Bayan na koma gida domin shan ruwa, sai yarona ya kira ni ta waya ya shaida min cewa wasu mutane ɗauke da bindigogi sun shigo kasuwa suna harbe-harbe.
“Sun tilasta Shugaban Kasuwa Alhaji Usman Yako ya fito daga motarsa suka kuma tafi da shi a cikin motarsu.”
Shi ma wani ɗan kwamitin kasuwar, Alhaji Abubakar Garba Karaye, ya ce: “Bayan mun idar da sallar Magriba a babban masallacin kasuwa, sai muka ji ƙarar harbe-harbe.
“Lokacin da muka leƙa, sai muka ga wasu mutane suna harbi a kusa da motar Shugaban Kasuwa.
“Bayan sun gama, suka ɗauke shi suka tafi da shi a cikin motarsu, sun bar tasa motar a kasuwa da harbin bindiga a jikinta.”
Shugabannin kasuwar sun ce ba a taɓa samun irin wannan hari tun bayan kafuwar kasuwar shekaru huɗu da suka gabata ba.
Sai dai kafin wanzuwar kasuwar, an yi ta samun rahoton wasu mutane da ake zargi suna ɓoyewa a cikin dazukan da ke kewayen kasuwar.
Har yanzu ba a samu jin ta bakin Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Oyo ba, domin ba ya ɗaukar waya.