Aminiya:
2025-04-13@04:56:20 GMT

Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira

Published: 21st, March 2025 GMT

Wata gobara da ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira na Munna Albadawi da ke ƙaramar hukumar Jere a Jihar Borno, ta lalata wasu gidaje 10 tare da salwantar da rayuwar yaro mai shekara 7 mai suna Abubakar Gargar.

A cewar shugaban sansanin, Babangida Mahmud gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 3:00 asubahin safiyar ranar 20 ga watan Maris, 2025, inda gobarar ta laƙume kayayyakin abinci da tufafi da dai sauran kayayyaki.

Taƙaddama: An kama wanda ya daɓa wa matarsa ​​wuƙa ta mutu ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe

Wanda kawo yanzu ba a tantance adadin asarar da ta haifar ba baya ga salwantar rai guda.

Hukumar kashe gobara ta Jihar Borno tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro sun yi nasarar shawo kan gobarar da ƙyar da jibin goshi bayan da ta yi ɓarna mai yawan gaske.

Tuni dai aka yi wa marigayin jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya shimfiɗa.

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar (SEMA) da sauran hukumomin jin ƙai sun baza jami’ansu a sansanonin don daidaita lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan gudun hijira Gobara a Maiduguri Munna Albadawi

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya yi wata muhimmiyar ganawar sirri da shugabannin sojojin Nijeriya a Abuja ranar Alhamis.

Taron wanda ya gudana daban-daban tare da babban hafsan sojin ƙasa, Laftanar Janar Olufemi Olatubosun Oluyede da babban hafsan sojin ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ikechukwu Ogalla da babban hafsan sojin sama, Air Marshal Hasan Bala Abubakar na shirin sake tura wani sabon yunƙuri na ɗaukar matakin haɗa kai kan maharan Boko Haram.

Sanƙarau: An tabbatar da ɓullar cutar ga mutane 300 a Sokoto An saki fasto an kuma tsare wanda ya kai kuɗin fansa

Majiyoyi daga taron sun bayyana cewa, tattaunawar ta ta’allaka ne kan ƙarfafa ayyukan soji a yankin Arewa maso Gabas, da inganta musayar bayanan sirri da magance yawaitar hare-haren da ’yan tada ƙayar baya ke yi a baya-bayan nan.

Gwamna Zulum a ranar Talatar da ta gabata, yayin wani taron tsaro da aka gudanar a Maiduguri, ya koka kan yawaitar hare-haren da ’yan ta’addan ke kai wa a cibiyoyin farar hula da na sojoji, inda ya yi kira da a ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki don kaucewa halin da ake ciki.

Zulum ya samu rakiyar Sanatoci masu wakiltar Borno ta Kudu, Mohammed Ali Ndume, Borno ta Arewa Mohammed Tahir Monguno da Borno ta tsakiya Barista Kaka Shehu Lawan.

Sauran a tawagar gwamnan sun haɗa da: Mukhtar Betera Aliyu da Injiniya Bukar Talba, ‘yan majalisar wakilai da Farfesa Usman Tar, kwamishinan yaɗa labarai da tsaron cikin gida na Jihar Borno.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji
  • MDD Ta Bukaci Taimako Dangane Rikicin Sudan Wanda Ya Isa Kasar Chadi
  • ‘Yan Boko Haram Na Ci Gaba Da Mamaye Sassan Jihar Borno -Zulum
  • Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji
  • Gobara Ta Ƙone Shaguna 12 A Kasuwar Siminti Ta Oyo
  • An Sace Dalibin Jami’ar Tarayya Birnin Kebbi
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 10, Sun Kashe Ɗan Bindiga 1 A Katsina