HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke
Published: 21st, March 2025 GMT
Jaridar “Yediot-Ahranot” ta buga wani rahoto da yake kunshe da gargadi daga jami’an sojan mamaya akan yadda ake samun koma baya na sojojin sa-kai saboda da dalilai mabanbanta.
Daga cikin dalilan da jaridar ta bijiro da su da akwai gajiya da yaki na lokacin mai tsawo da HKI ta shiga, sai kuma matsaloli na tattalin arziki da kashe kudade masu yawa wajen kula da su.
Haka nan kuma manyan jami’an sojan mamayar sun bayyana yiyuwar rusa rundunar sojan sa-kai din saboda babu wadanda su ka dace su jagorance ta, ga kuma tsadar tafiyar da rundunar kamar yadda jaridar ta “Ahranot” ta bayyana.
Ita kuwa jaridar “Financial-Times” ta bijiro da tata majiyar da take cewa; Yakin da ba shi da ranar karewa da Isra’ila take yi, ya gajiyar da sojojin sa-kai.
Wani sashe na rahoton jaridar ya ambaci cewa; Tare da cewa yarjejeniyar da aka yi da sojojin sa-kai din shi ne cewa a cikin shekara daya za su yi yakin kwanaki 30 ne kadai,amma kuma yanzu an sanar da iyalansu cewa, su kasance cikin shirin yin yaki babu kakkautawa har na tsawon shekaru masu yawa.
Jaridar ta “Financial Times” ta kuma ce ‘yan sahayoniyar suna da bukatar Karin sojoji 10,000 saboda kara tsaro, a yankunan da suke kusa da Gaza.
HKI tana da cikakkun sojoji170,000 sai kuma sojojin sa-kai da su ka kai 465, a 2024 kamar yadda shafin :Global Fire Power” ya ambata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas
Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi caccaki Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas.
Kwankwaso ya ce matakin da Tinubu ya ɗauka ya saɓa doka kuma barazana ne ga dimokuraɗiyya.
Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe NAJERIYA A YAU: Illar Sare Itatuwa Ga Sauyin Yanayi Da LafiyarmuA cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Kwankwaso ya gargaɗi cewa irin wannan matakin na iya kafa mummunan misali da kuma illata dimokuraɗiyya a Najeriya.
Kwankwaso, ya ruwaito yadda rikicin siyasa da ya haifar da soke zaɓen 1993, inda ya jaddada cewa ‘yan majalisa su daina ɓata lokacinsu kan abubuwan da ba su dace ba.
“Majalisa tana da alhakin sa ido kan ayyukan ɓangaren zartarwa, ba wai kawai yarda da duk abin da ta ce ba.
“Abu ne mai matuƙar tayar da hankali ganin yadda Majalisar Tarayya ta 10 ta fi kowace zama ‘yar amshin shata ga ɓangaren zartarwa,” in ji shi.
Tsohon gwamnan ya kuma soki yadda Majalisar Tarayya ta gaggauta amincewa da matakin Shugaba Tinubu ba tare da bin ƙa’idojin da kundin tsarin mulki ya tanada ba.
“Kundin tsarin mulki ya fayyace yadda ake yanke hukunci kan irin wannan matsala, amma ‘yan majalisa sun zaɓi amfani da murya wajen zaɓe, wanda hakan yana janyo shakku kan sahihancin lamarin.
“Gaggawar amincewa da dokar ta-ɓaci da zata kifar da gwamnatin da aka zaɓa, cin fuska ne ga dimokuraɗiyya,” in ji shi.
Kwankwaso ya kuma yi gargaɗi kan shigar sojoji cikin harkokin mulki, inda ya bayyana cewa hakan tamkar komawa baya ne bayan ci gaban da aka samu tsawon shekaru 26 na dimokuraɗiyya.
Ya bayyana damuwarsa cewa wannan matakin na iya zama wata dabara ta murƙushe jihohin da ba sa tare da jam’iyya mai mulki.
“A matsayinsa na wanda ke da’awar kare dimokuraɗiyya, Shugaba Tinubu ya kamata ya fi kowa fahimta cewa kawo sojoji cikin mulki hatsari ne.
“Wannan matakin ba wai kawai barazana ne ga zaman lafiya ba, yana iya zama hanyar kama-karya idan ba a dakatar da shi ba,” in ji Kwankwaso.