Cibiya Mai Fafutukar Kare Hakkokin Falasdinawa “Global 195” Ta Shelanta Farautar Sojojin HKI Da Su KaTafka Laifukan Yaki
Published: 21st, March 2025 GMT
Cibiyar ta “ Global 196” ta bakin babban shugabanta ta sanar da cewa a cikin watanni 18 da su ka gabata, ta tattara bayanai akan laifukan yakin da Isra’ila ta tafka a Gaza.” Haka nan kuma cibiyar mai matsuguni a Birtaniya ta ce, ya zuwa yanzu ta tattara da dalilai da su ka dace da ka’idojin shari’a a kotunan manyan laifuka na kasar.
Har ila yau cibiyar ta ce, bayan kammala tattara bayanai a zango na farko, za kuma ta bude shafi na gaba domin kara samun wasu bayanan da za su tabbatar da cewa an yi wa Isra’ilawan hukunci a cikin kasashen duniya, musamman masu dauke da zama ‘yan kasashe biyu.
Wani shiri da wannan cibiyar take da shi,shi ne na samar da wasu cibiyoyin a cikin nahiyoyin duniya da samar da ka’idoji ta fuskar shari’a da su ka dace da na duniya da kuma na kasashe domin farautar wadanda su ka aikata laifukan yaki a Gaza, da fitar da sammacin kamo su, saboda su fuskanci shari’a.
Wadanda wannan cibiyar take son ganin sun fuskanci shiri’a, sun hada jami’an sojan HKI, da ‘yan siyasa da duk masu hannu a aikata laifukan yaki.
Ita wannan cibiyar ta kunshi kawance na lauyoyi daga kasashen Malysia, Turkiya, Norway, Canada, Bosnia, da kuma Birtaniya.
Ana kuma sa ran cewa anan gaba wasu lauyoyin daga wasu kasashen duniya za su shiga ciki,musamman a wannan lokacin da HKI ta bude wani sabon kisan kiyashin akan al’ummar Falasdinu.
Cibiyar ta kasa da kasa mai son ganin an yi wa Falasdinawa adalci, ta kuma hada da fitaccen lauyan nan dan kasar Afirka Ta Kudu John Dugard, da kokarin jawo lauyoyi daga dukkakin kasashen duniya.
Cibiyar za ta yi aiki domin ganin a kowace jaha da gunduma ta kasashen duniya an samar da hanyar hukunta wadanda su ka aikata laifukan yaki a Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasashen duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Nijar, Burkina Faso da Mali sun fice daga kungiyar kasashe renon Faransa
Kasashen Nijar da Burkina Faso da kuma Mali kowannensu sun sanar da ficewa daga kungiyar kasashe renon faransa ta (OIF).
Nijar ta sanar da ficewa daga kungiyar a ranar Litini, yayin da Mali ta bi sahu a ranar Talata, aa daidai lokacin da ake raya makon kungiyar.
Babban sakataren ma’aikatar harkokin wajen kasar Laouali Labo, a wata wasika da ya aikewa jakadun kasar ya ce: “Gwamnatin Nijar ta yanke shawarar ficewa daga kungiyar ta OIF.”
Nijar dai na daga cikin kasashen da suka asassa kungiyar ta OIF, wacce aka kafa a Yamai babban birinin kasar a ranar 20 ga watan Maris na shekarar 1970, kuma tsohon shugaban kasar Dojori Hamani na waccen lokacin na daga cikin jagororin da suka kafa kungiyar.
To saidai dangankata ta yi tsami tsakanin faransa da sojojin dake mulki a kasashen guda uku a baya bayan nan.
Kungiyar ta OIF, “maimakon tallafawa wadannan kasashe wajen cimma manufofin raya al’ummarsu, (…) ta kauce wa hanya inda ta sanya siyasa a cikin lamuranta,” in ji ministocin harkokin wajen kawancen kasashen guda uku na Sahel a wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar a yammacin jiya Talata.
Kungiyar ta OIF, da ta hada kasashe da gwamnatoci 93, manufarta ita ce inganta harshen Faransanci da raya al’adu, don ƙarfafa zaman lafiya, da dimokuradiyya da ‘yancin dan adam, don tallafawa ilimi, horo da bincike, da kuma inganta hadin gwiwar tattalin arziki don samun ci gaba mai dorewa.
Sai nan da watanni shida masu zuwa ne ficewar kasashen za ta tabbata.