HausaTv:
2025-03-22@01:48:28 GMT

Sojojin Sudan Sun Kwace Iko Da Fadar Shugaban Kasa A Birnin Khartum

Published: 21st, March 2025 GMT

Sojojin Sudan sun sanar a yau Juma’a cewa sun kwace iko da fadar shugaban kasa dake tsakiyar birnin Khartum, bayan da su ka kori mayakan rundunar kai daukin gaggawa.

Majiyar ta ce, sojojin na Sudan sun fara da kutsawa cikin fadar shugaban kasar ne, ta mashigar gabas,bayan da su ka kashe mayakan rundunar kai daukin gaggawa da dama,yayin da wasu da dama su ka gudu zuwa cikin kasuwar dake kusa.

Bayanin da sojojin na Sudan su ka fitar ya kunshi cewa; Mun murkushe mayakan Duqlu, ‘yan ta’adda a tsakiyar birnin Khartum da kuma kasuwar Larabawa da ginin fadar shugaban kasa da sauran ma’aikatu.”

Har ila yau majiyar sojan na Sudan ta ce,su kuma yi nasarar rusa makamai da motocin yakin rundunar kai daukin ggagawar,kamar kuma yadda ta kame wasu masu maya.

Janar Nabil Abdullah wanda shi ne kakakin sojan na Sudan ya sanar da cewa; Za su ci gaba kai hare-hare a cikin dukkanin fagagen yaki har samun nasara.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An kori shugaban hukumar leken asiri ta cikin gidan Isra’ila

Gwamnatin Isra’ila ta sanar da korar shugaban hukumar liken asiri ta cikin gidan kasar Ronen Bar, wanda Firaministan kassar Benjamin Netanyahu ya ce bai gamsu da kwarewarsa ba hasali ma ba’a yarda da shi.

 “Gwamnati baki daya ta amince da shawarar Firaminista Benjamin Netanyahu na kawo karshen wa’adin” Ronen Bar, wanda zai bar ofis idan aka nada magajinsa ye zuwa ranar 10 ga watan Afrilu, in ji ofishin Firayim Minista a cikin wata sanarwa.

Rashin gamsuwa da aikin na kokaren shugaban hukumar ta Shin-bet, ta fito fili a baya bayan bayan bayannan da suke fitowa game da harin kungiyar Hamas na ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

Ronen Bar, wanda aka nada a watan Oktoba 2021 na wa’adin shekaru biyar, ya tabbatar tun kafin yanke hukuncin cewa zai kare kansa a gaban “hukumomin da suka dace”.

A cikin wata wasika da ya aikewa jama’a da yammacin Alhamis, ya bayyana cewa dalilan da suka sa aka kore shi daga aiki, wanda Benjamin Netanyahu ya sanar a ranar Lahadi, ya dogara ne da “sha’awar kansa” da nufin “hana bincike kan al’amuran da suka shafi harin ranar 7 ga Oktoba da wasu muhimman batutuwa da Shin Bet ke bincikar su.”

Dama shugaban hukumar ya amince kwanan baya da gazawar hukumar da ayek jagoranta wajen hana harin na Hamas.

A cikin wata sanarwa da aka fitar kwanan baya, shugaban hukumar ta Shin Bet, Ronen Bar, ya amince da cewa, hukumar ta ” gaza a cikin aikinta” na dakile ayyukan Operation Al-Aqsa, tare da kutsawa manyan sansanonin Isra’ila bayan da sojoji da ‘yan sandan gwamnatin suka yi kaca-kaca da su, kuma y ace ya dauki nauyin gazawar a wuyansa.

Hukumar ta amince da gagarumin gibi a cikin tattara bayanan sirri da kuma dogaro da matakan kariya da ake da su, wanda ya haifar da rashin fahimtar kungiyar Hamas, tare da sauran kungiyoyin gwagwarmaya.

Wannan na zuwa ne kwanaki bayan wani “binciken cikin gida” ya nuna cewa, an gaza wajen dakile harin na Hamas.

Binciken da sojojin Isra’ila suka gudanar ya soki yadda gwamnatin kasar ke dogaro da bayanan sirri da kuma raina karfin Hamas, kura-kuran da suka haifar da mummunan sakamako ga gwamnatin Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke
  • Dubban Mutane Sun Fito Zanga-Zangar Yin Allawadai Da Kama Magajin Garin Istambul
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Yaffa Kusa Da Tel Aviv A Karo Na Biyu A Cikin Sa’o’i 24
  • An Bukaci Shugaban Kasa Ya Sa Ido Ga Aikin Biyan Kudaden Fansho
  • An kori shugaban hukumar leken asiri ta cikin gidan Isra’ila
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
  • ’Yan bindiga sun sace shugaban kasuwar kayan miya ta Akinyele a Oyo
  • Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin Ribas 
  • Sojojin Kasar Yemen Sun Kai Wa HKI Hari Da Makami Mai Linzami