’Yan bindiga sun hallaka matashi ana sallar Tahajjud a Kaduna
Published: 22nd, March 2025 GMT
Wasu da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne sun kai hari wani masallaci da ke yankin Tudun Wada a Jihar Kaduna, inda suka kashe wani matashi yayin da ake tsaka da sallar Tahajjud.
Sai dai rundunar ’yan sandan jihar, sun kama mutum 12 da ake zargi da hannu a kai hari masallacin da ke Tudun Wada a Ƙaramar Hukumar Kaduna ta Kudu.
Kakakin rundunar, Mansir Hassan, ya ce maharan sun fito daga wurare daban-daban kamar Malalin Gabas, Tudun Wada, Rafin Guza, da Unguwar Baduko.
Sun kai farmaki Masallacin Layin Bilya, titin Makwa a Rigasa da misalin ƙarfe 2 na dare yayin da masu mutane ke sallar Tahajjud.
Kafin jami’an tsaro su isa wajen, maharan sun sun daɓa wa wani matashi mai shekara 28, Usman Mohammed, wuƙa har lahira.
Rundunar tare da haɗin gwiwar JTF sun ɗauki mataki cikin gaggawa, inda suka kama mutum 12 kuma ana bincike a kansu.
Haka kuma, an samu makamai a hannu waɗanda aka kama.
An fara bincike domin gano gaskiyar lamarin da tabbatar da cewa an hukunta waɗanda suka aikata laifin.
Sakamakon haka, ’yan sanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a wuraren ibada da sauran wuraren da ake ganin za su iya fuskantar barazana.
Hukumomi sun buƙaci al’umma da su kasance masu sanya ido tare da gaggauta kai rahoto idan sun ga wani abun zargi.
’Yan sanda sun kuma gargaɗi ’yan ta’adda da su daina aikata laifuka ko su fuskanci hukunci mai tsanani.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hari Sallar Tahajjud Tudun Wada
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina
Dakarun Sojin Najeriya sun kuɓutar da mutum 84 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a Ƙaramar Hukumar Kankara a Jihar Katsina.
Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na jihar, Nasir Mu’azu, ya bayyana cewa sojojin runduna ta 17 tare da tallafin jiragen yaƙi sun kai farmaki maɓoyar ’yan ta’adda da ke yankin Sanusi Dutsin-Ma da tsaunukan Pauwa.
’Yan bindiga sun sace shugaban kasuwar kayan miya ta Akinyele a Oyo Farashin fetur na iya tashi bayan Dangote ya daina sayar da mai a NairaYa ce a yayin farmakin dakarun sun kashe wasu daga cikin ’yan bindiga sannan suka kuɓutar da waɗanda aka sace.
Daga cikin mutanen da aka ceto, akwai maza bakwai, mata 23, da yara 54.
Kwamishinan ya ce gwamnatin jihar ta yaba wa sojojin bisa ƙoƙarinsu, kuma tuni aka samar da abinci da kulawa ga mutanen da aka kuɓutar, kafin a mayar da su ga iyalansu.
Ya ƙara da cewa Gwamnatin Katsina ba za ta yi sulhu da ’yan ta’adda ba, domin tana da niyyar ci gaba da yaƙi da su har sai an daƙile matsalar garkuwa da mutane a jihar.