Aminiya:
2025-03-23@19:44:16 GMT

Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum

Published: 22nd, March 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Borno, ta ɗauki matakin hukunta wasu ma’aurata, Mamman Sheriff da matarsa, da aka kama suna cin zarafin wata yarinya a unguwar Pompomari Bypass da ke Maiduguri.

Bayan bayyanar faifan bidiyon da ya nuna ma’auratan suna dukan yarinyar, mutane da dama sun yi tir da abin a shafukan sada zumunta.

Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia

Wannan ya sa Hukumar Tsaron Sibil Difens (NSCDC) ta cafke su nan take.

Gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum, ya tabbatar da cewa gwamnati ba za ta musu sassauci ba.

Ya ce ma’aikatun shari’a, ilimi, da harkokin mata sun haɗa kai domin ganin an hukunta waɗanda suka aikata laifi.

Yarinyar, wacce ɗaliba ce, ta shiga harabar gidan ma’auratan domin tsinkar mangwaro bayan tashi daga makaranta, inda suka yi mata dukan kawo wuƙa.

A halin yanzu tana kwance a asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), inda Dokta Lawan Bukar Alhaji ya ɗauki nauyin jinyarta.

Gwamnatin Borno ta kuma tallafa wa iyayen yarinyar da kayan agaji, abinci, da kuɗi.

Iyayenta da sauran jama’a sun yaba wa gwamnatin kan matakin da ta ɗauka na kare haƙƙin yarinyar.

Gwamnati ta jaddada cewa duk wanda aka kama da cin zarafin yara ba zai tsira daga hukunci ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cin zarafi Ɗaliba gwamnati Ma aurata Mangwaro yarinya

এছাড়াও পড়ুন:

An Bukaci Shugaban Kasa Ya Sa Ido Ga Aikin Biyan Kudaden Fansho

An bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya tabbatar da sa ido sosai kan yadda aka fitar da kudade naira biliyan 758 domin warware duk wasu basussukan fensho da ake bin su domin hana yin zagon kasa.

 

A cikin wata sanarwa da kungiyar Muslim Media Watch Group ta fitar, kodineta na kasa, Alhaji Ibrahim Abdullahi ya kuma yabawa shugaba Tinubu kan matakin da ya dauka na ragewa ‘yan fansho na tarayya daga halin kuncin da suke ciki.

 

A cewar sanarwar, dole ne a sanya ido sosai kan sabuwar manufar domin hana duk wani zagon kasa daga wasu Ma’aikatan Asusun Fansho (PFA) da ake zargi da batawa wasu ‘yan fansho da suka yi rajista da su rai.

 

Ya bayyana cewa wasu Ma’aikatan Asusun Fansho sun kara wa ‘yan fansho matsalolin da suke fuskanta ta hanyar jinkirta biyan su fansho kusan shekaru 2 bayan sun yi ritaya.

 

Ta ce duk irin wadannan laifuffuka da rashin iya aiki sun karfafa cin hanci da rashawa a sassan al’umma na tattalin arzikin kasa.

 

Sanarwar ta yi kira da a samar da cikakken tsari da ingantaccen tsarin sa ido daga fadar shugaban kasa da hukumar fansho ta kasa PENCOM wajen magance matsalolin ‘yan fansho gaba daya.

 

Tana kira ga Gwamnonin Jihohi a fadin Tarayya da su yi koyi da Gwamnatin Tarayya wajen biyan basussukan da ake bin Jihohi da Kananan Hukumomi.

 

Sanarwar ta kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta yin la’akari da yin kwaskwarima ga dokokin gudanar da shari’ar laifuka (ACJ) domin hukunta laifukan tattalin arziki da ake tafkawa a Najeriya.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • Araghchi : Ya kamata Duniyar Musulmi ta dauki mataki mai karfi kan Isra’ila
  • Mata sun ƙwace kasuwancin kayan lambu a Gombe
  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • Falasdinawa 80,000 ne suka halarci sallar Juma’a a mako na uku na Ramadan a masallacin Al-Aqsa
  • Gwamnoni Na Kamun Kafa A Wurin Tinubu Don Hana Bai Wa Kananan Hukumomi ‘Yanci
  • An Bukaci Shugaban Kasa Ya Sa Ido Ga Aikin Biyan Kudaden Fansho
  • Gwamnatin Yobe na ciyar da almajirai a Tsangayu 85 kullum