An yi wa wata karya tiyatar ceton rai
Published: 22nd, March 2025 GMT
Wata karya ta hadiyi safa 24 da sauran kayan sawa, inda suka makale masa a mukamuki – lamarin da ya haifar da yi masa tiyatar ceton rai a Jihar California a Amurka, kamar yadda cibiyar kula da dabbobi ta bayyana.
Wata karya mai suna Luna, jinsin Bernese Mountain da ta shafe wata 7 tana fama da rashin lafiya, sakamakon hadiye wasu kayayyaki na mamallakinta a ranar 16 ga Fabrairu bayan kamar yadda Cibiyar Ba da Agajin Dabbobi ta Corona ta ce a cikin wani sakon da ta wallafa a Instagaram.
Lokacin da ta fara amai, an garzaya da ita zuwa asibitin dabbobi, inda wani likitan dabbobi ya bude cikinta, ya cire tufafin da ya haifar da toshewar hanjinta.
“Lokacin da ‘yan uwan masu karyar suka lura tana amai kuma tana cikin rashin lafiya mai tsauri, sai suka garzayo da ita wurinmu,” in ji cibiyar.
“Ba tare da bata lokaci ba, yanzu Luna yanzu ta fara kada wutsiyarta!” Ta kara da cewa “karyar tana da tsananin son safa “.
Cibiyar kula da lafiyar dabbobi ta saka hoton safa da aka cire daga hanjin karyar tare da hotunan D-ray na toshewar hanjinta, a cewar kafar Storyful, wanda ya fara gano labarin ceton karyar.
Wasu hotuna sun nuna Luna – tana wasa – cikin farin ciki da kwanciyar hankali a kan gadon asibiti, bayan an yi mata tiyata.
Cibiyar ta yi gargadin cewa, wadanda suka mallaki karnuka idan suka “lura suna amai, ko alamar rashin lafiya” sai su yi sauri su tuntubi likitan dabbobi.”
“Ita wannan karyar ta musamman ce, kuma muna farin cikin samun labarin murmurewarta,” in ji wani sakon da wani ya wallafa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
Jami’an tsaro sun samu nasarar kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ake kira Gwaska Ɗan Ƙarami da wasu mayaƙa 100 a Jihar Katsina.
Kwamishinan Harkokin Cikin Gida na Jihar Katsina, Dokta Nasir Mu’azu ya bayyana matakin a matsayin wata gagarumar nasara a yaƙi da ’yan bindiga ake yi a jihar.
An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba — Ganduje“Abin farin ciki ne ga jihar, domin wannan nasara ta taimaka wajen wargaza ayyukan ’yan bindigar da ke addabar garuruwa da ƙauyukan da ke ƙananan hukumomin Faskari da Kankara da Bakori da Malumfashi da kuma Kafur,” in ji Kwamishinan.
Ya bayyana cewa runduna ta 17 ta sojin Nijeriya tare da ɓangaren sojin saman ƙasar ne suka ƙaddamar da hare-haren a ranar 10 ga watan Afrilun shekarar 2025 a dabar ɓarayin daji a Mununu Bakai da Zango da Jeka Arera da Malali, da kuma Ruwan Godiya duka a cikin ƙananan hukumomin Kankara da Faskari.
Haɗin gwiwar jami’an tsaron ƙasar ne suka ƙaddamar da harin a ranar Juma’a wanda ya yi sanadin kisan Gwaska — wanda ya kasance mataimakin shahararren ɗan bindiga Malan, shugaban ISWAP a yankin Arewa Maso Yamma.
“Hare-haren da suka yi daidai kan ɓarayin, bisa bayanan sirrin da aka samu, sun yi silar kashe wani wanda ake nema ruwa-a-jallo da aka fi sani da Gwaska, wanda mataimaki ne ga wani shugaban ’yan bindiga mai alaƙa da ISWAP,” in ji shi.
“Bayanan sirri sun tabbatar da cewa kwanan nan ne Gwaska ya yi ƙaura daga Ƙaramar Hukumar Danmusa zuwa dajin Munumu.
Rahotonni sun ce sojojin sun lalata maɓoyar ’yan bindigar da dama a sassan jihar a lokacin harin, tare da ƙwato da kuma lalata wasu manyan bindigogi masu jigida da waɗanda aka ƙera a cikin gida.
Harin na zuwa ne bayan da a farkon mako ’yan bindigar suka yi garkuwa da mutum 43 mazauna ƙauyukan Maigora da ke yankin Ƙaramar Hukumar Dandume.
Kazalika, dakarun tsaro sun ƙaddamar da wani aiki da sanyin safiyar ranar 10 ga watan Afrilun shekarar 2025, a hanyar da ɓarayin daji ke bi a Dutsen Wori gefen hanyar Dandume zuwa Kandamba, da ke wajen garin Dandume a kan iyaka da ƙananan hukumomin Faskari da Sabuwa.
Aikin da aka aiwatar da misalin ƙarfe 3:45 na dare ya yi silar kashe ɓarayi shida ciki har da shugabansu, yayin da sauran ɓarayin suka tsere da raunukan bindiga.
Bayanai sun nuna cewa dakarun sun ƙwace mashina bakwai yayin da saura huɗu suka tsere cikin daji.
An bi sawun ɓarayin ne daga dabarsu da ke Maigora/Doroyi cikin Ƙaramar Hukumar Faskari.