Kyari ya ci gaba da cewa, wannan bangare na noma don samun riba; shi ma zai amfana da Naira biliyan 500, wanda ya kai kimanin dala biliyan 300, wanda su ma wadannan kudaden za a bai wa Bankin Aikin na Noma.

Kazalika, Kyari ya yi kira ga Bankin EBRD, da ya zuba hannun jari a fannin aikin noman kasar, domin kasar ta cimma burin da ta sanya a gaba, musamman domin Nijeriya ta rage asarar da take yi a yayin girbin amfanin gona da samar da kayan aikin noman rani da sauran makamantansu.

Dakta Heike Harmgart, Manajan Daraknatan Bankin na EBRD da ke kula da yankin Afirka, wadda kuma ta jagoranci tawagar a nata jawabin ta ce, tawagar ta kawo ziyara ne ga Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci na kasar nan ne, sakamakon Nijeriya a kwanan baya ta zuba shaya ko hannun jari, domin gano bangarorin da ya kamata Bankin EBRD ya zuba hannun jarinsa a fannonin tattalin arzikin kasar.

Ta kara da cewa, Bankin na EBRD, zai yi aiki da Bankunan kasar nan; domin kara bunkasa zuba kudade a fannin aikin nomar kasar, inda ta ce; Bankin zai kuma bude ofishinsa a Jihar Legas.

“Muna kuma shirin daukar ‘yan Nijeriya masu hazaka, a bangarorin tattalin arzikin kasa, kuma a taron da za mu gudanar a watan Mayu na shekara-shekara, za mu gabatar da takardar bukata ga Nijeriya, kan bangarorin da za mu zuba hannun jari a kasar”, in ji Dakta Heike.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar

A ci gaba da shimfida ikonsu da suke yi a cikin birnin Khartum, sojojin Sudan sun kwace iko da babban bankin kasar, kwana daya bayan da su ka kori dakarun kai daukin gaggawa daga fadar shugaban kasa.

Kamfanin dillancin labarun “Reuters” ya nakalto majiyar sojojin Sudan tana cewa; A yau Asabar sun yi nasarar kwace iko da babban bankin kasar, tare kuma da shimfida ikonsu a cikin wasu yankunan na birnin Khartum.

Kakakin sojan kasar Sudan Nabil Abdullah, ya bayyana cewa; Mun rusa sojoji da kayan aikin abokan gaba. Haka nan kuma Abdullah ya sanar da kwace wasu ma’aikatu da suke a tsakiyar birnin Beirut da su ka kasace a karkashin ikon dakarun kai daukin gaggawa.

Ana zargin rundunar kai daukin gaggawa da tafka laifukan yaki a cikin yankunan da a baya su ka shimfida ikonsu a ciki, har da babban birnin kasar Khartum.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  • Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar
  • Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99
  • Kasar Sin Ta Bayar Da Rijiyoyin Burtsasai 66 Ga Al’ummomin Zimbabwe Dake Fama Da Karancin Ruwa
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i
  • Hajjin Bana: Dole A Yi Wa Maniyyatan Bauchi Riga-kafin Foliyo – Hukumar Alhazai
  • IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya
  • An Bukaci Shugaban Kasa Ya Sa Ido Ga Aikin Biyan Kudaden Fansho
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Taimakon NAMA Don Gudanar Da Aikin Hajjin Bana Cikin Nasara