Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
Published: 23rd, March 2025 GMT
A kokarin Gwamnatin Jihar Jigawa na karfafa ayyukan noman rani tare da samar da wadataccen abinci da inganta rayuwa, ta kaddamar da shirin noman rani na Lallashi da ake amfani da rijiyoyin burtsatse a Karamar Hukumar Maigatari ta jihar.
Rahoton na nuna cewa, an yi aikin ne domin canza salon noman rani da sauran ayyukan noma a yankunan da galibi hamada ce.
A cewar rahoton, wannan shiri ana yin amfani da makamashin hasken rana da kuma amfani da na’urori masu rahusa tare da dabarun noman rani don samar da harkokin noman rani mai inganci cikin sauki.
Dakatar da Gwamnan Ribas zubar da ƙimar Nijeriya ne a idon duniya — Jonathan An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a NijarDa yake jawabi a lokacin kaddamar da aikin, Gwamna Umar Namadi ya bayyana muhimmancin aikin, inda ya bayyana hakan a matsayin wata hanya ta jaddada kudirin gwamnatinsa na ganin an samar da abinci mai yalwa da samar da hanyoyin rayuwa mai dorewa da rage radadin talauci a tsakanin al’umma.
Ya kuma bayyana cewa, babban abin da gwamnatinsa ta sanya a gaba shi ne na cimma manufofin kudirorinta 12 wajen amfani da hanyoyin noma na zamani a Jihar Jigawa, musamman ta hanyar gudanar da ayyukan noma a duk shekara.
Ya kara da cewa, gwamnatinsa na daukar matakai daban-daban don gyara da fadada wuraren noman rani a fadin jihar da suka hada da samar da madatsun ruwa da rijiyoyin burtsatse na yau da kullum.
Sai dai an bayyana cewa shirin noman na Lallashi da rijiyar burtdatse ya kunshi gonaki hekta 10 kuma yana samun tallafin manyan rijiyoyin burtsatse irin na masana’antu guda hudu, kuma ya zuwa yanzu, manoma sama da 80 ne ke cin gajiyar shirin kai-tsaye, wanda ake sa ran zai bunkasa noman sosai da kuma yaukaka tattalin arziki.
Da yake jawabi a madadin manoman yankin, malam Aliyu Musa ya bayyana cewa, abin da gwamnati ke yi wa al’ummomin da ke kewayen wurin noman rijiyoyin burtsatse tamkar jari ta bayar na rayuwa da ba za a iya tantance adadinsa ba.
A cewarsa, jama’a za su ci gaba da addu’o’in samun nasarar shirin tare da fadada shirin domin kara fadada shi a yankunan jihar gaba daya.
“Da farko mutanen wannan yanki suna yin noman rani ne da zarar lokacin damina ya kare, amma labarin ya canza a yanzu, wanda ke nufin ba za a bar kauye zuwa birni ba don ci-rani.
“Nan ba da dadewa ba birni zai zo gare mu, yayin da muka fara nazarin wannan dama mai albarka ta tashi a matsayin al’ummomin da ke da wuraren noman rani,” inji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Jigawa Malam Umar Namadi
এছাড়াও পড়ুন:
Araghchi : Iran za ta mayar da amsa ga wasikar Trump cikin kwanaki masu zuwa
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya bayyana cewa, Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta mayar da martani ga wasikar shugaban Amurka Donald Trump a cikin kwanaki masu zuwa ta hanyoyin da suka dace.
Araghchi ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi kai tsaye a gidan talabijin na Jamhuriyar Musulunci ta Iran (IRIB) jiya Alhamis.
Araghchi ya kuma lura cewa a wannan karon, ci gaban ya zo tare da wani yunkuri na diflomasiyya daga Amurkawa, ciki har da wasika da bukatar yin shawarwari.
Ya kuma bayyana cewa manufar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a bayyane take. “Ba za mu shiga tattaunawa kai tsaye karkashin matsin lamba, barazana, ko karin takunkumi.”
A cewar Araghchi, tilas ne a gudanar da shawarwari bisa daidaito da kuma kyakkyawan yanayi.
Ministan harkokin wajen kasar ya kuma bayyana cewa wasikar “mafi yawan barazana ce,” amma kuma akwai damamaki a ciki.
“Mun yi nazari sosai kan dukkan bangarorin wasikar, tare da yin la’akari da kowane daki-daki sosai,” in ji shi.
A farkon watan Maris ne Trump ya bayyana cewa ya rubuta wasika zuwa ga Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.
A karshen watan Fabrairu, Ayatullah Khamenei, a wata ganawa da jami’an sojin sama a Tehran, ya bayyana cewa bai ga amfanin tattaunawa da Amurka saboda ba zata warware matsaloli ba.
Kalaman nasa sun zo ne sa’o’i bayan da gwamnatin ta Trump ta kakaba wa Iran takunkumai da Trump ya bayayana da “mafi girman matsin lamba” kan Iran.