Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-24@04:28:42 GMT

Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare

Published: 23rd, March 2025 GMT

Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare

Gwamnatin Jihar Jigawa ta sake jaddada bukatar bin dokar da ta hana kiwon dare da makiyaya ke yi a fadin jihar domin rage hadurra a tituna, wanda ke haddasa asarar rai ko shiga mawuyacin hali a sanadiyar raƙuman da ke bi ta manyan tituna.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan yayin da ya karbi bakuncin tawagar Kungiyar Makiyayan Raƙuma ta Yammacin Afirka a ziyarar girmamawa da suka kai Fadar Gwamnati a Dutse.

 

Ya ce gwamnatin ta himmatu matuka wajen ganin ta kula da lafiyar al’ummar jihar.

Malam Umar Namadi ya kara da cewa, wannan gwamnati tana da masaniya kan haramtattun ayyukan wasu makiyaya, musamman waɗanda ke shigowa daga ƙasashe makwabta.

Ya bayyana shirin gwamnatin jihar na yin rajistar makiyaya domin sauƙaƙa samunsu
idan buƙatar hakan ta taso.

Namadi ya nuna damuwarsa kan yawan asarar rayuka da raunuka daban-daban da jama’a ke fuskanta sakamakon yawaitar raƙuma da ke tsallaka manyan hanyoyi kowacce rana.

A nasa jawabin, babban sakataren Kungiyar Makiyayan Yammacin Afirka a Najeriya, Abubakar Mustapha Andaza, ya ce sun kai ziyarar ne domin su gabatar da kansu ga gwamnan, tare da neman shawarwarin gwamnatin jihar kan yadda za su gudanar da harkokinsu yadda ya dace.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa

Wata kungiya mai suna Grassroots Mobilizers for Better Nigeria Initiative (GMBNI), ta yi Allah wadai da kisan gilla da aka yi wa wani  Almajiri a ƙaramar hukumar Gwaram, Jihar Jigawa.

Ƙungiyar ta bayyana matuƙar bakin ciki da ɓacin rai game da wannan cin zarafin da aka yi wa yaron, wanda ya kai ga mutuwarsa cikin mawuyacin hali.

A cewar jami’in yankin Arewa maso Yamma na kungiyar ta GMBNI, Abbas Rufa’i Wangara, rahotanni sun nuna cewa wani Malamin makarantar Allo ya yi wa yaron bulala da har ta kai ga mutuwarsa.

Lamarin ya ƙara muni  inda ake zargin Malamin ya yanke kan gawar  yaron, ya cire mazakutarsa gabansa na sirri, sannan ya binne gawar a wani ƙaramar rami.

GMBNI ta bayyana wannan aika-aika a matsayin cin zarafin ɗan Adam.

Ƙungiyar ta miƙa ta’aziyyarta ga iyalan mamacin, tana mai jaddada cewa babu wani yaro da ya kamata ya fuskanci irin wannan zalunci, musamman a wurin da ake koyar da ilimi da tarbiyya.

GMBNI ta nanata buƙatar gaggawar yin gyara a tsarin ilimin Almajiranci, wanda ya daɗe yana fama da sakaci, cin zarafi, da rashin kulawa.

Ta yi kira ga hukumomi a dukkan matakai da su ɗauki matakan da suka dace don kare Almajirai tare da tabbatar da sun sami ingantaccen ilimi cikin kyakkyawar kulawa.

Ƙungiyar ta kuma bukaci hukumomin tsaro da na shari’a da su gudanar da cikakken bincike kan lamarin, tare da tabbatar da cewa an hukunta wanda ya aikata wannan danyen aiki ba tare da ɓata lokaci ba.

Shugabar GMBNI, Ambasada (Dr.) Fatima Mohammed Goni, ta sake jaddada aniyar ƙungiyar na kare haƙƙin yaran da ke cikin mawuyacin hali.

Ta yi kira ga ƙungiyoyin farar hula, ‘yan kasa da al’ummar duniya baki ɗaya da su haɗa kai wajen neman adalci ga mamacin da kuma tashi tsaye wajen tabbatar da  adalci da daidaito ga dukkan yara a Najeriya.

Usman Mohammed Zaria

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
  • Dalilan Gwamnatin Tarayya Na Zuba Naira Tiriliyan 1.5 A Bankin Aikin Noma -Kyari
  • Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum
  • GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
  • Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai
  • Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa
  • Gwamnatin Yobe na ciyar da almajirai a Tsangayu 85 kullum
  • Babu ’yan adawan da za su iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027 — Ganduje