Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
Published: 23rd, March 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta sake jaddada bukatar bin dokar da ta hana kiwon dare da makiyaya ke yi a fadin jihar domin rage hadurra a tituna, wanda ke haddasa asarar rai ko shiga mawuyacin hali a sanadiyar raƙuman da ke bi ta manyan tituna.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan yayin da ya karbi bakuncin tawagar Kungiyar Makiyayan Raƙuma ta Yammacin Afirka a ziyarar girmamawa da suka kai Fadar Gwamnati a Dutse.
Ya ce gwamnatin ta himmatu matuka wajen ganin ta kula da lafiyar al’ummar jihar.
Malam Umar Namadi ya kara da cewa, wannan gwamnati tana da masaniya kan haramtattun ayyukan wasu makiyaya, musamman waɗanda ke shigowa daga ƙasashe makwabta.
Ya bayyana shirin gwamnatin jihar na yin rajistar makiyaya domin sauƙaƙa samunsu
idan buƙatar hakan ta taso.
Namadi ya nuna damuwarsa kan yawan asarar rayuka da raunuka daban-daban da jama’a ke fuskanta sakamakon yawaitar raƙuma da ke tsallaka manyan hanyoyi kowacce rana.
A nasa jawabin, babban sakataren Kungiyar Makiyayan Yammacin Afirka a Najeriya, Abubakar Mustapha Andaza, ya ce sun kai ziyarar ne domin su gabatar da kansu ga gwamnan, tare da neman shawarwarin gwamnatin jihar kan yadda za su gudanar da harkokinsu yadda ya dace.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari
Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya ziyarci tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari a Kaduna.
Atiku ya samu rakiyar tsofaffin gwamnoni da suka haɗa da tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da tsohon Gwamnan Sokoto Aminu Waziri Tambuwal da wasu jiga-jigan ’yan siyasa.
An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojojiKamar yadda aka wallafa bidiyon ziyarar a Shafin Atiku na Facebook, an rubuta cewa sun ziyarci Buharin, kuma sun sha dariya.
“A matsayina na Wazirin Adamawa, na tsaya domin gudanar da shagungulan Sallah a Adamawa, inda na wakilci Sarkin Adamawa, Lamiɗo Fombina a wasu shagulgulan.
“Yau kuma na kai ziyarar gaisuwar Sallah ga Muhammadu Buhari wanda ya shugabanci ƙasar a tsakanin 2015 zuwa 2023. Na ji daɗin ziyarar, saboda kamar yadda ya saba, ya yi ta ba mu dariya sai da haƙarƙarina suka yi zafi.” Cewar Atiku.