Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar
Published: 23rd, March 2025 GMT
Iran, ta yi Allah wadai da harin ta’addancin da ya yi sanadin mutuwar gomman mutane a wani masallaci a kudu maso yammacin Jamhuriyar Nijar.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya yi kakkausar suka kan harin da aka kai wa masallata.
Akalla mutane 44 ne suka mutu yayin da 13 suka jikkata a harin da aka kai a kauyen Fonbita da ke cikin kauyan Kokorou dake jihar Tillabery wanda ya faru a lokacin da wasu ‘yan ta’addan na kungiyar Da’ish a yankin Sahara (ISGS) suka far wa masallacin, inda suka auka wa masu ibada dake sallar Juma’a.
Baghaei ya bayyana cewa, wannan ta’addancin da aka aikata a lokacin sallar Juma’a ya saba wa ka’idar Musulunci, kuma ya saba wa dukkanin ka’idojin shari’a da hakkin dan Adam na kasa da kasa.
Kakakin na Iran ya jaddada muhimmancin kara inganta hadin gwiwa a matakai daban-daban na shiyya-shiyya da na kasa da kasa don dakile da yaki da ta’addanci.
Ya zama dole a gurfanar da masu hannu a harin ta’addanci da kuma hukunta su.
Baghaei ya nuna juyayi ga iyalan wadanda harin ya rutsa da su da gwamnati da kuma al’ummar Nijar kan harin ta’addanci.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harin ta addanci
এছাড়াও পড়ুন:
An yi wa Jakadan Afirka ta Kudu da Amurka ta kora tarbar Jamurumai bayan komawarsa gida
Ebrahim Rasool, jakadan Afirka ta Kudu da gwamnatin Trump ta kora, ya samu tarba a wannan Lahadin daga daruruwan magoya bayansa da suke rera wakoki domin karrama shi a filin jirgin sama na Cape Town.
Jama’a sun kewaye Rasool da matarsa Rosieda bayan isowarsu, yayin da ‘yan sanda suka yi musu rakiya har zuwa tashar jirgin kasa.
Da yake yiwa magoya bayansa jawabi, Rasool ya ce, Abin da ya faru yana a matsayin wulakanta ku ne ku al’ummar Afirka ta kudu, amma kuma idan kuka tsaya tsayin daka kan manufofinku na ‘yancin kai to za ku ci gaba da rayuwa a cikin mutunci da daukaka.
Ya ce ba laifi muka yi ba, ammam kuma mun dawo gida ba tare da nadama ba.
Gwamnatin Trump ta kori Rasool sakamakon kalaman da ya yi a cikin shafukan yanar gizo, wanda gwamnatin Trump ke kallon kalamansa a matsayin batunci ga Amurka.
Korar Rasool, wanda tsohon mai fafutukar yaki da wariyar launin fata ne, ya kara dagula dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, wadanda manufofin Trump na baya-bayan nan suka kara kawo tankiya da zaman doya da manja a tsakaninsu.